Sojojin HKI Sun Ce Ba Zasu Fita Daga Wurare 5 A Kudancin Kasar Lebanon Ba
Published: 18th, February 2025 GMT
Sojojin HKI Sun Bada sanarwan cewa ba zasu bar wasu tuddai guda 5 a kudancin kasar Lebanon ba, har zuwa wani lokacin da basu sani ba, saboda tsaron haramtacciyar kasar.
Tashar talabijin ta Almayadin ta kasar Lebanon, ta nakalto cewa tankunan yakin HKI sun kutsa cikin garin kafarshuba na kudancin kasar Lebanon kuma sun kafa sansanin sojojin a garin.
A jiya litinin ce yakamata sojojin HKI su fice daga kudancin kasar Lebanon da suka mamaye, amma a jiyan din ne suka bada sanarwan cewa ba zasu fita daga wurare 5 daga kudancin kasar ta Lebanon ba.
Kafin haka bayan kwanaki 60 da tsagaita budewa juna wuta ne, yakamata sojojin HKI su fice daga kudancin kasar ta Lebanon, amma tare da shiga tsakani na gwamnatin kasar Amurka, gwamnatin kasar Lebanon ta tsawaita wanzuwar sojojin yahudawan har zuwa yau Talata 18 ga watan Fabrayrun shekara ta 2025. A yau ne yakamata sojojin kasar Lebanon su karbi dukkan wuraren da sojojin yahudawan suke mamaye da su a kudancin kasar.
Har yanzun dai ba’a ji ta bakin gwamnatin kasar Lebanon dangane da wannan al-amarin.
Mai magana da yawan sojojin HKI sojojinsa ba zasu fita daga wadannan wurare 5 ba sabaoda tsaron HKI kuma a duk lokacinda suka ga mutanensu a yankin arewacin HKI zasu sami amince da zaman lafiya suna iya ficewa daga wadannan wurare.
Kafin haka dai babban sakatarin kungiyar Hizbullah Sheikh Na’im Qasim ya bayyana cewa sojojin HKI basu da wani uzuri na ci gaba da kasancewa a kudancin kasar Lebanon daga yau Talata 18 ga watan Fabrayrun shekara ta 2025
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: a kudancin kasar Lebanon
এছাড়াও পড়ুন:
Fursunoni 12 Sun Tsere Daga Gidan Yari A Jihar Kogi
Gwamnatin jihar ta yi kira ga al’umma da su ba da hadin kai ga jami’an tsaro ta hanyar bayar da bayanai da za su taimaka wajen kamo sauran fursunonin da suka tsere.
Haka kuma, an buƙaci dangin waɗanda suka tsere da su mika kansu ga hukuma domin guje wa hukunci mai tsanani.
Wannan ba shi ne karo na farko da ake samun irin wannan matsala ba, domin a baya an samu fursunoni sun tsere daga gidajen yari daban-daban a Nijeriya.
Hakan na nuni da buƙatar ƙara tsaurara matakan tsaro a gidajen gyaran hali domin hana faruwar irin haka a gaba.
A halin yanzu, jami’an tsaro na ci gaba da bincike tare da ƙoƙarin kamo sauran fursunonin da suka tsere domin tabbatar da tsaro da zaman lafiya a yankin.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp