Babban kwamandan sojojin kasar Iran ya bayyana cewa: Sun sabunta hanyoyin da sojojin Iran zasu mayar da martani kan duk wani harin wuce gona da iri kamar yadda Jagoran juyin juya halin Musulunci ya bada umarni

Babban kwamandan sojojin kasar Iran Manjo Janar Abdur-Rahim Mousawi ya bayyana cewa: Tun tsawon kwanaki da suka gabata jagoran juyin juya halin Musuluncin ya bayyana cewa: Idan Amurka ta farma tsaron al’ummar Iran, to lallai Iran za ta kai farmaki kan tsaronta ba tare da wata shakka ba, wannan ya kasance umarni ne bayyananne ga dakarun Iran, kuma kwamandojin sun sabunta shirinsu na aiwatar da wannan umarni, kuma a halin yanzu Iran a shirye take tsaf don gudanar da umarni a aikace.

Manjo Janar Mousawi ya kara da cewa: Sun sha wahalhalu da dama, kuma makiyansu sun yi kokari da dukkan karfinsu a cikin shekaru 46 da suka gabata don dakile juyin juya halin Musulunci da ruguza shi da karkatar da alkiblarsa, amma wannan al’umma karkashin jagorancin Jagoran juyin juya halin Musulunci da jinin shahidan ta, ta ci nasara kan dukkanin wadannan makirce-makircen da alfahari da nasara.

Mousawi ya jaddada cewa: Su al’umma ce da ke cewa sun nisanta daga karbar wulakanci, kuma sun yi alkawari ga Allah Madaukakin Sarki, da jagoransu da kasarsu mai albarka da kuma al’ummarsu masu zurfin hankali da basira gami da hakuri da jinin shahidan Iran 200,000, wadanda suka yi shahada, da Falasdinawa sama da 50,000, da suka yi shahada a Gaza da jinin Sayyed Hassan Nasrullahi da Sayyed Hashim Safiyyullah da Imad Mughniya da Isma’il Haniyya da Yahaya Al-Sinwar,   cewa za su ci gaba da gwagwarmaya da kalubalantar mamayar mulkin mallakar Amurka har sai ta mika wuya kuma ta mutunta hakkokin al’ummomi.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: juyin juya halin

এছাড়াও পড়ুন:

Jakadan Sin A Amurka: Mayar Da Karin Haraji Makami Kaikayi Ne Da Zai Koma Kan Mashekiya

A jiya Asabar 22 ga watan nan, jakadan kasar Sin a Amurka Xie Feng, ya amsa gayyatar halartar taro na 2 na tattaunawar sassan Sin da na Amurka game da batun tattalin arziki karkashin cibiyar Jimmy Carter, inda ya gabatar da jawabi ta kafar bidiyo. 

A cikin jawabinsa, jakada Xie Feng ya ce ko kadan, hadin gwiwar Sin da Amurka bai taba zama na wani fanni ya ci riba dayan ya yi asara ba. Maimakon haka, kaso 41 bisa dari na kamfanonin Amurka dake kasar Sin na daukar Sin a matsayin kasa ta biyu a duniya, wajen samun ribar hada hadar kasuwanci.

Dole Gwamnatin Tarayyar Nijeriya Ta Daina Barazana Ga Masu Sukar Ta – Amnesty An Kashe Askarawa 6 da ‘Yan Sa-kai 4 A Zamfara 

Xie ya kara da cewa, matakin Amurka na mayar da batun kara haraji wani makami na neman biyan bukata, zai zamo tamkar “kaikayi da zai koma kan mashekiya”. Ya ce Sin a shirye take ta dauki matakai na warware damuwar juna ta hanyar tattaunawa da gudanar da shawarwari, bisa daidaito da martaba juna, amma maimakon haka Amurka na nacewa ga dorawa Sin laifi, tana kokarin dakile ta da nuna danniya, sai dai kuma a nata bangare, Sin za ta dauki dukkanin matakai da suka wajaba don kare hakkoki da moriyarta.

Daga nan sai Xie Feng ya jaddada cewa, wajibi ne Sin da Amurka su saba, su kuma ci karo da juna a wasu fannoni. Amma jigon daidaita hakan shi ne kaucewa keta hurumin moriyar juna, da kaucewa keta muradun juna. Ya ce goyon bayan “’yancin kan Taiwan” tsoma baki ne cikin harkokin gidan kasar Sin, kuma amincewa da “’yancin kan Taiwan” mataki ne na gurgunta zaman lafiya a zirin Taiwan. Yayin da kokarin amfani da batun yankin Taiwan wajen juya kasar Sin ba zai yi nasara ba, a daya hannun mataki ne mai matukar hadari. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Masanin Amurka: Matakan Kariyar Cinikayya Da Amurka Ke Aiwatarwa Babban Kuskure Ne
  • Jakadan Sin A Amurka: Mayar Da Karin Haraji Makami Kaikayi Ne Da Zai Koma Kan Mashekiya
  • Gwamnatin Kano Ga Ma’aikata: Duk Mai Bukatar Aikinsa Dole Ya Gabatar Da Kansa A Wajen Tantancewa
  • Iran ta yi Allah-wadai da harin ta’addanci da aka kai a wani masallaci a kudu maso yammacin Nijar
  • Sudan: Sojoji na ci gaba karbe mahimman gine-gine a birnin Khartoum
  • Kwana Daya Bayan Kwace Fadar Shugaban Kasa, Sojojin Sudan Sun Kwace Babban Bankin Kasar
  • Ranar Mata Ta Duniya: NPA Ta Mayar Da Hankali Wajen Kare ‘Yancin Mata –Dantsoho
  •  HKI: Ana Samun Koma Bayan Sojojin Sa-Kai Da Suke
  • Jagora: Amurka Ta Kwana Da Sanin Cewa Ba  Wata Riba Da Za Ta Ci Ta Hanyar Yi Wa  Iran Barazana
  • Gobara Ta Kashe Yaro A Sansanin ‘Yan Gudun Hijira A Maiduguri