Yadda Fim Din “Ne Zha 2” Ya Samu Matukar Karbuwa A Duniya Bai Zo Da Mamaki Ba
Published: 18th, February 2025 GMT
Yawan kudin tikitin kallon fim din “Ne Zha 2” na kasar Sin da aka saya ya zarce dala biliyan 16 a daren jiya, abin da ya sa ya shiga sahun fina-finai 9 mafi samun yawan kudin tikitin kallon fim dake sahun gaba a duniya. Dalilin da ya sa fim din samun wannan ci gaba shi ne ingancin abin da ya kunsa.
Labarin da wannan fim ya gabatar ya yi daidai da wasan yanar gizo mai suna “Black Myth: Wukong”, wanda shi ma na kasar Sin ne.
Idan aka duba bangaren fasahar zamani ta wannan fim, za a ga cewa, an kwashe shekaru 5 ana tsara fim din na “Ne Zha 2”, wanda ya kunshi hotuna na musamman kusan 2,000 da wasu abubuwa na musamman masu tasiri a shirin fim sama da 10,000. Matakin da ya nuna cewa, fina-finan Cartoon da Sin ta kirkiro ba kawai sun amfani da fasahar waje ba, har ma a yanzu sun iya zama ma’aunin da za a yi misali da shi.
Ban da wannan kuma, fim din ya bayyana dankon zumuncin iyali da abokai masu nuna zaman tare da zuciya daya, kuma ya nuna yadda mutanen fim din suka yi iyakacin kokarinsu wajen kare garinsu da iyalansu, abin da ya dace da nagartaccen tunanin Bil-Adama na bai daya. Shi ya sa fim din ya zama mai taba zuciyar masu kallo na kasa da kasa. Abin da kuma har ila yau ya nuna cewa, zuciyoyin Bil-Adama a kusa suke da juna, wadda hakan ke iya daidaita mabambantan ra’ayoyin al’adu a tsakanin kasashe daban-daban, da kara mu’amala da cudanyar al’ummun duniya. (Amina Xu)
এছাড়াও পড়ুন:
Atiku ya jagoranci manyan ’yan siyasa sun ziyarci Buhari
Tsohon Mataimakin Shugaban Nijeriya kuma ɗan takarar shugaban ƙasa a 2023, Alhaji Atiku Abubakar ya ziyarci tsohon shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari a Kaduna.
Atiku ya samu rakiyar tsofaffin gwamnoni da suka haɗa da tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai da tsohon Gwamnan Sokoto Aminu Waziri Tambuwal da wasu jiga-jigan ’yan siyasa.
An gano gawar makiyayi da ƙwato shanu a Filato Boko Haram: Zulum ya yi ganawar sirri da Shugabannin sojojiKamar yadda aka wallafa bidiyon ziyarar a Shafin Atiku na Facebook, an rubuta cewa sun ziyarci Buharin, kuma sun sha dariya.
“A matsayina na Wazirin Adamawa, na tsaya domin gudanar da shagungulan Sallah a Adamawa, inda na wakilci Sarkin Adamawa, Lamiɗo Fombina a wasu shagulgulan.
“Yau kuma na kai ziyarar gaisuwar Sallah ga Muhammadu Buhari wanda ya shugabanci ƙasar a tsakanin 2015 zuwa 2023. Na ji daɗin ziyarar, saboda kamar yadda ya saba, ya yi ta ba mu dariya sai da haƙarƙarina suka yi zafi.” Cewar Atiku.