Yadda Fim Din “Ne Zha 2” Ya Samu Matukar Karbuwa A Duniya Bai Zo Da Mamaki Ba
Published: 18th, February 2025 GMT
Yawan kudin tikitin kallon fim din “Ne Zha 2” na kasar Sin da aka saya ya zarce dala biliyan 16 a daren jiya, abin da ya sa ya shiga sahun fina-finai 9 mafi samun yawan kudin tikitin kallon fim dake sahun gaba a duniya. Dalilin da ya sa fim din samun wannan ci gaba shi ne ingancin abin da ya kunsa.
Labarin da wannan fim ya gabatar ya yi daidai da wasan yanar gizo mai suna “Black Myth: Wukong”, wanda shi ma na kasar Sin ne.
Idan aka duba bangaren fasahar zamani ta wannan fim, za a ga cewa, an kwashe shekaru 5 ana tsara fim din na “Ne Zha 2”, wanda ya kunshi hotuna na musamman kusan 2,000 da wasu abubuwa na musamman masu tasiri a shirin fim sama da 10,000. Matakin da ya nuna cewa, fina-finan Cartoon da Sin ta kirkiro ba kawai sun amfani da fasahar waje ba, har ma a yanzu sun iya zama ma’aunin da za a yi misali da shi.
Ban da wannan kuma, fim din ya bayyana dankon zumuncin iyali da abokai masu nuna zaman tare da zuciya daya, kuma ya nuna yadda mutanen fim din suka yi iyakacin kokarinsu wajen kare garinsu da iyalansu, abin da ya dace da nagartaccen tunanin Bil-Adama na bai daya. Shi ya sa fim din ya zama mai taba zuciyar masu kallo na kasa da kasa. Abin da kuma har ila yau ya nuna cewa, zuciyoyin Bil-Adama a kusa suke da juna, wadda hakan ke iya daidaita mabambantan ra’ayoyin al’adu a tsakanin kasashe daban-daban, da kara mu’amala da cudanyar al’ummun duniya. (Amina Xu)
এছাড়াও পড়ুন:
Syria: SOHR ta fallasa jami’an tsaron sabuwar gwamnati na yi tsiraru kisan gilla
Kungiyar da ke sa ido da kare hakkin dan adam ta Syria (SOHR) ta fitar da fayafan bidiyo guda hudu da ke dauke da hotunan azabtarwa da kisa da jami’an tsaron sabuwar gwamnatin kasar karkashin kungiyar Tahrir Sham suke aiwatarwa a kan fararen hula tsiraru marasa rinjaye a kasar.
Kungiyar da ke sa ido kan kare hakkin bil adama a Syria ta bayyana a ranar Lahadi cewa, ta samu faifan bidiyo guda hudu ne da ke nuna yadda ake aiwatar da hukuncin kisa kan wasu matasa da ba sa dauke da makamai daga ‘yan Alawiyya, da jami’an tsaro suka aiwatar a kauyen al-Shir da ke yankin Latakia a ranar 7 ga watan Maris.
A cewar kungiyar, faifan bidiyon ya kara tabbatar da yadda aka aiwatar da kisan gillar da aka yi a yankunan gabar tekun Syria da kuma wadanda suka aikata hakan a kan fararen hula.
A cikin faifan bidiyo na farko ya nuna wasu matasa biyu sun durkusa a kasa yayin da jami’an tsaron sabuwar gwamnatin Syria suke zaginsu tare da lakada musu matsanancin duka, duk kuwa da ikirarin da suka yi na cewa ba su aikata wani laifi ba.
A cikin wani faifan bidiyo na biyu, an nuna yadda aka azabtar da wasu fararen hula hudu ciki har da tsofaffi biyu, da kuma tilasta wa daya daga cikinsu sumbaci takalmin wani jami’in tsaro.
Kaset na uku ya nuna irin mumunan duka da aka yi wa fararen hula da bindigogi da karafa kafin daga baya kuma duk aka kashe su.
Dukkanin wadanda suka aikata wadannan munannan laifuka dai sabbin jami’an tsaron sabuwar gwamnatin Syria ne da kungiyar Tahrir Sham mai dangantaka da kungiyar Alqaida ta kafa a Syria bayan hambarar da gwamnatin Bashar Assad.