Za a binciki INEC kan jinkirin gudanar da zaɓen cike giɓi
Published: 18th, February 2025 GMT
Majalisar Wakilai ta umarci kwamitinta kan harkokin zaɓe da ya binciki Hukumar Zaɓe ta Ƙasa INEC dangane da jinkirin da take yi na gudanar da zaɓen cike giɓin wasu kujerun ’yan majalisar tarayya da na jihohi.
Majalisar a wannan Talatar ta kuma bayyana cewa jazaman ne kwamitin ya gayyaci Hukumar INEC domin ta bayar da dalilai kan tsaikon da aka samu da kuma yadda take ƙoƙarin yi wa tufkar hanci.
Aminiya ta ruwaito cewa Majalisar ta buƙaci kwamitin ya sauke wannan nauyi tare da miƙa mata rahoton bincikensa nan da makonni huɗu.
Wannan dai na zuwa ne bayan ƙorafin da wani ɗan majalisar, Jafaru Leko ya gabatar yana mai kafa hujja da Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya wanda ya ɗora wa INEC alhakin gudanar da zaɓe a faɗin ƙasar.
Kazalika, ya naƙalto sassa na 47 da 90 da ke cikin Kundin Tsarin Mulkin wanda ya hukunta assasa majalisun tarayya da na jihohi a matsayin wani rukuni na ’yancin ’yan ƙasa su samu wakilci.
Ya yi ƙorafin cewa tun bayan Zaɓen 2023 da waɗanda suka biyo baya, an samu giɓi a majalisun tarayya da na jihohi saboda wasu dalilai kamar mutuwa, karɓar wasu muƙaman ko ajiye aiki.
Jafara Leko ya ci gaba da ƙorafin cewa Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya ya yi tanadin gudanar da zaɓen cike giɓi cikin tsawon lokacin da bai gaza wata guda ba da samun giɓin.
Ya ƙara da cewa, gudanar da zaɓen wanda alhakinsa ya rataya a wuyan Hukumar INEC shi ne zai tabbatar da wakilcin kowace mazaɓa a ƙasar.
A cewarsa, wannan jinkiri da INEC take ci gaba da yi rashin biyayya ne ga Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya, lamarin da ke cutar da al’umma ko mazaɓar da ba su wakilci a hukumance.
Aminiya ta ruwaito cewa, a halin yanzu akwai kujerun ’yan Majalisar Tarayya bakwai masu giɓi da suka haɗa da na Majalisar Wakilai biyar da kuma biyu a Majalisar Dattawa.
Kujerun da ke da giɓi a Majalisar Wakilan sun haɗa da na jihohin Edo, Oyo, Kaduna, Ogun da Jigawa sai kuma na Majalisar Dattawa da suka ƙunshi Edo da Anambra.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Majalisar Wakilai Zaɓe Kundin Tsarin Mulkin gudanar da zaɓen a Majalisar
এছাড়াও পড়ুন:
Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kaduna Ya Yi Bikin Easter Tare da Al’ummomin Kiristoci
Makera, Jihar Kaduna – Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kaduna, Rt. Hon. Yusuf Dahiru Liman, ya halarci bukukuwan Easter tare da al’ummomin Kiristoci na Gundumar Makera, inda ya bukaci su yi amfani da lokacin wajen tabbatar sa saƙon bangaskiya, yabo, da sadaukarwa da ke tattare da bikin.
A jawabin da ya gabatar, Hon. Liman ya jaddada muhimmancin bikin Easter a matsayin lokaci na sabunta dogaro da Allah. Ya kuma bukaci mabiya addinin Kirista da su rungumi koyarwar hakuri, kauna, da kuma fifita bukatun wasu akan nasu.
Kakakin ya kuma yi kira ga daukacin jama’ar Jihar Kaduna da su ci gaba da bunkasa zaman lafiya da juna ba tare da la’akari da bambancin addini, kabila ko ra’ayin siyasa ba, yana mai cewa hadin kai shi ne ginshikin ci gaban jihar da kasa baki daya. Ya jaddada bukatar gudanar da addu’o’i don dorewar zaman lafiya da inganta sha’anin tsaro.
A kokarinsa wajen inganta kiwon lafiya, Hon. Yusuf Dahiru Liman ya dauki nauyin mutane 200 da suka hada da tsofaffi da mabukata daga Kakuri-Gwari da unguwar Television domin shiga tsarin inshorar lafiya na KACHMA wanda ke ba da damar samun kulawar lafiya mai araha.
Baya ga hakan, Kakakin ya bayar da guraben karatu ga dalibai 200 daga wadannan al’ummomi domin tallafa musu a harkar ilimi da gina al’umma mai wayewa.
Bikin na Easter ya samu halartar shugabannin addini da sarakuna, shugabannin matasa da mata, da sauran manyan masu ruwa da tsaki na al’umma.
A nasa jawabin, Kwamishinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida na Jihar Kaduna, Mr. James Kanyip ya yabawa nasarorin da aka samu wajen karfafa tsaro da inganta zaman tare a jihar. Ya bayyana cewa gwamnati na amfani da hanyoyin sasantawa da tattaunawa wajen magance matsalolin tsaro, tare da kira ga jama’a da su kasance masu lura da kuma sanar da hukumomi duk wani abin da ba su amince da shi ba.
Shugabannin al’umma su ma sun yi amfani da damar wajen yabawa Kakakin bisa kokarinsa na kawo ci gaba. Mista Monday Kazah daga Kakuri-Gwari da Mista Ishaya Amfani daga unguwar Television sun jinjinawa Hon. Liman saboda shirye-shiryensa na tallafawa jama’a ta hanyar bayar da guraben karatu, koyar da sana’o’i, da samar da ayyukan yi. Sun kuma tabbatar masa da goyon baya da addu’o’i domin samar da dokokin da za su bunkasa rayuwar jama’a.
Shamsuddeen Mannir Atiku