Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-02-21@14:20:02 GMT

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alhinin Rasuwar Edwin Clark

Published: 18th, February 2025 GMT

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alhinin Rasuwar Edwin Clark

 

Gwamnatin Tarayya tayi matukar alhinin rasuwar Dattijo kuma Tsohon Kwamishinan Yada Labarai na Tarayya, Cif Edwin Clark, wanda ya rasu yana da shekaru casa’in da bakwai.

 

Ministan Yada Labarai da Wayar da Kan Jama’a, Mohammed Idris, ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da aka rabawa manema labarai a Abuja.

 

Ya ce, Marigayi Cif Clark gwarzo ne mai kishin kasa, mai fafutukar tabbatar da adalci da gaskiya, kuma ginshiki ne a ci gaban dimokuradiyyar Najeriya.

 

Mohammed Idris, ya kara da cewa, Marigayi ya sadaukar da kansa wajen bautawa kasa a fannoni da dama, musamman a matsayin shi na ɗan siyasa da mai kishin kasa, wanda ya bar gagarumar alama a harkokin mulki, hadin kai, da ci gaban Najeriya.

 

“Fafutukarsa da hikimarsa da jajircewarsa wajen ci gaban kasa sun sa, ya zama murya mai matukar tasiri a siyasar Najeriya,” in ji Minista.

 

“Za a yi matukar rashin shawarwarinsa masu hikima da gudunmawarsa wajen gina kasa.”

 

“Muna mika ta’aziyyarmu ga iyalan Cif Clark, gwamnatin da al’ummar Jihar Delta, da dukkan ‘yan Najeriya da suka amfana da rayuwarsa mai albarka. Muna rokon Allah Ya jikansa, Ya kuma bai wa iyalansa da duk masu jimamin wannan rashi babban hakuri da karfin zuciya.”

 

Rel/Adamu Yusuf

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Clark Gwamnatin Rasuwar Tarayya

এছাড়াও পড়ুন:

Jakadan Sin Dake Najeriya Ya Gana Da Karamar Ministar Harkokin Wajen Kasar

Jakadan Sin dake kasar Najeriya Yu Dunhai ya gana da karamar ministar harkokin waje ta kasar Bianca Odumegu-Ojukwu.

Jakada Yu ya bayyana cewa, a shekarar bara, shugaban kasar Sin Xi Jinping da shugaban kasar Najeriya Bola Tinubu, sun sanar da inganta dangantakar dake tsakanin Sin da Najeriya zuwa dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare a dukkan fannoni, wanda ya zama babban ci gaba ga raya dangantakar dake tsakanin kasashen biyu. A farkon shekarar bana kuma, memban hukumar kula da harkokin siyasa ta kwamitin tsakiya na jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin kuma ministan harkokin wajen kasar Wang Yi ya kai ziyara Najeriya cikin nasara, hakan ya kara kyautata dangantakar dake tsakanin kasashen biyu zuwa sabon matsayi. A cewar jakadan, Sin tana son hada shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya da manufar fatan samun farfadowa ta Najeriya, da kara hadin gwiwa bisa manufofin raya kasashen biyu, da raya manufar makomar bai daya ta Sin da Najeriya mai inganci, yana mai cewa, ta hakan za su taka muhimmiyar rawa wajen sa kaimi ga hadin gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa a duniya.

A nata bangare, madam Bianca Odumegu-Ojukwu ta bayyana cewa, shugaba Tinubu ya kai ziyara kasar Sin a shekarar bara, lamarin da ya shaida cewa, Najeriya tana maida hankali ga raya dangantakar dake tsakaninta da Sin. Ta ce kasar Najeriya ta tsaya tsayin daka kan manufar Sin daya tak, kuma tana son hada hannu da kasar Sin wajen aiwatar da ayyukan da aka cimma a ganawar shugabannin kasashen biyu da taron koli na dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka na Beijing, ta yadda za a inganta hadin gwiwar kasashen biyu har ya amfanawa jama’arsu baki daya. (Zainab Zhang)

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaba Tinubu Ya Yaba Da Gudunmawar Da IBB Ya Bayar Yayin Mulkinsa
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar Da Shirin Da’awah Na Mata A Jihar Jigawa
  • Jakadan Sin Dake Najeriya Ya Gana Da Karamar Ministar Harkokin Wajen Kasar
  • NAJERIYA A YAU: Tanadin Dokar Kasa Kan Kirkirar Gwamnatin Bibiya A Kano
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa; Yahudawan Sahayoniyya Sun Kasa Murkushe Gwagwarmaya
  • Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alhinin Rasuwar Dattijon Kasa, Edwin Clark
  • Gwamnatin Niger Ta Hana Yan Najeriya Dauke Da Passpor Ta Na ECOWAS Shiga Kasar
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bai Wa Jihar Jigawa Kayayyakin Noma Na Sama Da Naira Biliyan 5
  • Yadda Fim Din “Ne Zha 2” Ya Samu Matukar Karbuwa A Duniya Bai Zo Da Mamaki Ba