Aminiya:
2025-03-23@22:16:02 GMT

DAGA LARABA: Dalilan Da ’Yan Najeriya Ke Haɗa Buga-Buga Da Aikin Albashi

Published: 19th, February 2025 GMT

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Yanayin tattalin arziki da ma wasu dalilai kan tilasta wa mutane da dama, ciki har da masu karɓar albashi a karshen wata, neman wata hanya ta daban dake kawo Karin kudade.

Shin mene ne yake kawo hakan, kuma mene ne tasirinsa a kan rayuwar masu buga-bugar da ma al’umma?

NAJERIYA A YAU: Ci-gaban Da Hukumomin Raya Shiyyoyi Za Su Samar DAGA LARABA: Dalilan Da Al’adar Zanen Fuska Ke Neman Gushewa A Kasar Hausa

Shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi duba ne a kan irin buga-bugar da ’yan Najeriya suke yi don sama wa kansu mafita.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Za a hukunta ma’auratan da suka ci zarafin yarinya a kan mangwaro — Zulum

Gwamnatin Jihar Borno, ta ɗauki matakin hukunta wasu ma’aurata, Mamman Sheriff da matarsa, da aka kama suna cin zarafin wata yarinya a unguwar Pompomari Bypass da ke Maiduguri.

Bayan bayyanar faifan bidiyon da ya nuna ma’auratan suna dukan yarinyar, mutane da dama sun yi tir da abin a shafukan sada zumunta.

Majalisar Wakilai ta musanta karɓar kuɗi kan dokar ta-ɓaci a Ribas Mace ta farko ta zama shugabar ƙasar Namibia

Wannan ya sa Hukumar Tsaron Sibil Difens (NSCDC) ta cafke su nan take.

Gwamnan jihar, Babagana Umara Zulum, ya tabbatar da cewa gwamnati ba za ta musu sassauci ba.

Ya ce ma’aikatun shari’a, ilimi, da harkokin mata sun haɗa kai domin ganin an hukunta waɗanda suka aikata laifi.

Yarinyar, wacce ɗaliba ce, ta shiga harabar gidan ma’auratan domin tsinkar mangwaro bayan tashi daga makaranta, inda suka yi mata dukan kawo wuƙa.

A halin yanzu tana kwance a asibitin Koyarwa na Jami’ar Maiduguri (UMTH), inda Dokta Lawan Bukar Alhaji ya ɗauki nauyin jinyarta.

Gwamnatin Borno ta kuma tallafa wa iyayen yarinyar da kayan agaji, abinci, da kuɗi.

Iyayenta da sauran jama’a sun yaba wa gwamnatin kan matakin da ta ɗauka na kare haƙƙin yarinyar.

Gwamnati ta jaddada cewa duk wanda aka kama da cin zarafin yara ba zai tsira daga hukunci ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Matasa sun kashe yaron da suka yi garkuwa da shi a Bauchi
  • EFCC Ta Cafke Mutum 21 Bisa Zarginsu Da Zambar Intanet A Bauchi
  • Matasa 4 Sun Yi Garkuwa Da Yaro, Sun Kashe Shi A Bauchi
  • Dalilan Gwamnatin Tarayya Na Zuba Naira Tiriliyan 1.5 A Bankin Aikin Noma -Kyari
  • Za a hukunta ma’auratan da suka ci zarafin yarinya a kan mangwaro — Zulum
  • Sallah: Tinubu Ya Raba Wa ’Yan APC Buhun Shinkafa 7,000 A Zamfara
  • IAR da NAERLS Sun Shirya Taron Tattaunawa Da Masu Ruwa Da Tsaki Kan Noma Dawa A Najeriya
  • An Bukaci Shugaban Kasa Ya Sa Ido Ga Aikin Biyan Kudaden Fansho
  • NAJERIYA A YAU: Illar Sare Itatuwa Ga Sauyin Yanayi Da Lafiyarmu
  • MAGGI: Girke-girken Ramadan masu kawo sauyi da zumunta