HausaTv:
2025-04-13@09:52:24 GMT

Gwamnatin Niger Ta Hana Yan Najeriya Dauke Da Passpor Ta Na ECOWAS Shiga Kasar

Published: 19th, February 2025 GMT

Gwamnatin Jumhuriyar Nijer daga jiya Talata ta fara aikin hana yan Najeriya dauke da Passport na kungiyar ECOWAS shiga kasar.

Kafin haka dai mutane daga kasashen ECOWAS suna shiga kasashen kungiyar ba tare da bukatar visar shiga ko wace kasa daga cikin kasashe kungiyar ba.

Amma bayan da kasashe 3 Nijer, Burkina Faso da kuma Mali suka fice daga kungiyar sannan suka samar da sabon Passport a tsakanin kasashen uku, sai al-amura suka fara sauyi tsakaninu da Ecowas.

Sun fara hana wadanda suke rike da Passpory na kasashen ECOWAS shiga kasashen ba tare da visa ba.

Gwamnatin Nijer bata bada sanarwan fara aiki da wannan dokar ba. Kuma wani jami’in shige da fice na Niger ya ce umurnin ne aka basu.

A bangaren Najeriya kuma gwamnatin kasar ta ce bata da masaniyya dangane da hakan. Amma za ta fara bincike don tabbatar da yadda al-amarin yake.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Xi Jinping Zai Ziyarci Kasashen Vietnam Da Malaysia Da Cambodia

Ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ta sanar da cewa, bisa gayyatarsa da sakatare janar na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Vietnam kuma shugaban jamhuriyar gurguzu ta Vietnam ya yi, shugaban kasar Sin Xi Jinping, zai kai ziyarar aiki kasar daga ranar 14 zuwa 15 ga wata.

 

Haka kuma, bisa gayyatarsa da firaministan kasar Malaysia da sarkin Cambodia suka yi, shugaban na kasar Sin kuma sakatare janar na JKS, zai ziyarci kasashen Malaysia da Cambodia daga ranar 15 zuwa 18 ga wata. (Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kallo Daya Mutum Za Yi Min Ya Gane Masana’antar Kannywood Ta Canza Rayuwata -Farida Abdullahi
  • Xi Jinping Zai Ziyarci Kasashen Vietnam Da Malaysia Da Cambodia
  • Tawagogin gwamnatin Kongo da kungiyar M23 sun isa  Doha domin tattaunawa
  • Namibiya ta janye bizar shiga ga wasu manyan kasashe na duniya
  • Gwamnatin Sakkwato na biyan mafi ƙarancin albashin N70,000 – NLC
  • Iran Da Armenia Suna Fara Atisayen Hadin Giwa Don Karfafa Tsaron   Kan Iyakar Kasashen Biyu
  • Kasashen China Da EU Sun Maida Martani Kudin Fito Kan Kasar Amurka
  • Sin Ta Nuna Damuwa Kan Mummunan Tasirin Harajin Kwastam Na Amurka A Taron WTO
  • Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Taron Kolin CELAC Karo Na 9
  • ECOWAS ta damu da takun-tsaka tsakanin Aljeriya da Mali