HausaTv:
2025-03-23@23:02:51 GMT

Gwamnatin Niger Ta Hana Yan Najeriya Dauke Da Passpor Ta Na ECOWAS Shiga Kasar

Published: 19th, February 2025 GMT

Gwamnatin Jumhuriyar Nijer daga jiya Talata ta fara aikin hana yan Najeriya dauke da Passport na kungiyar ECOWAS shiga kasar.

Kafin haka dai mutane daga kasashen ECOWAS suna shiga kasashen kungiyar ba tare da bukatar visar shiga ko wace kasa daga cikin kasashe kungiyar ba.

Amma bayan da kasashe 3 Nijer, Burkina Faso da kuma Mali suka fice daga kungiyar sannan suka samar da sabon Passport a tsakanin kasashen uku, sai al-amura suka fara sauyi tsakaninu da Ecowas.

Sun fara hana wadanda suke rike da Passpory na kasashen ECOWAS shiga kasashen ba tare da visa ba.

Gwamnatin Nijer bata bada sanarwan fara aiki da wannan dokar ba. Kuma wani jami’in shige da fice na Niger ya ce umurnin ne aka basu.

A bangaren Najeriya kuma gwamnatin kasar ta ce bata da masaniyya dangane da hakan. Amma za ta fara bincike don tabbatar da yadda al-amarin yake.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

EFCC Ta Cafke Mutum 21 Bisa Zarginsu Da Zambar Intanet A Bauchi

Jami’an Hukumar Yaki da Masu Yi Wa Tattalin Arzikin Kasa Zagon Kasa (EFCC) na shiyyar Gombe, sun kama wasu mutane 21 da ake zargi da damfarar Intanet a Jihar Bauchi.

A cewar wata sanarwa da hukumar ta wallafa a shafinta na Facebook a ranar Litinin, “An kama wadanda ake zargin ne ta hanyar samun sahihan bayanan sirri kan zargin da ake yi musu na damfarar Intanet a yankin Kaure New Government Reservation Area, Bauchi da Awala, a titin Maiduguri, Jihar Bauchi.

Gwamnatin Tarayya Ta Karbi Rukunin Farko Na Taraktoci Dubu Biyu Daga Belarus Matasa 4 Sun Yi Garkuwa Da Yaro, Sun Kashe Shi A Bauchi

“Abubuwan da aka kwato daga hannunsu a wajen kama su sun hada da motoci kirar BMW daya da Toyota Camry, PlayStation 5 guda uku, wayoyi masu tsada 30, da babbar talabijin daya, injin PoS guda shida, iPad guda hudu, da kwamfyutoci biyar.”

Sanarwar ta ce za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu da zarar an kammala bincike.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Al-Huthi Ya Ce Kawo Wani Jirgin Ruwa Mai Daukar Jiragen Saman Yaki Gazawa Ce Ga Amurka
  • Araghchi : Ya kamata Duniyar Musulmi ta dauki mataki mai karfi kan Isra’ila
  • EFCC Ta Cafke Mutum 21 Bisa Zarginsu Da Zambar Intanet A Bauchi
  • Wang Yi: Kasar Sin Na Da Kwarin Gwiwa Kan Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Japan Da Koriya Ta Kudu  
  • Chelle Ya Fara Da Ƙafar Dama A Super Eagles 
  • Za a hukunta ma’auratan da suka ci zarafin yarinya a kan mangwaro — Zulum
  • Chelle Ya Fara Da Ƙafar Dama A Super Eagles
  • Cibiya Mai Fafutukar Kare Hakkokin Falasdinawa “Global 195” Ta Shelanta Farautar Sojojin HKI Da Su KaTafka Laifukan Yaki
  • Gwamnoni Na Kamun Kafa A Wurin Tinubu Don Hana Bai Wa Kananan Hukumomi ‘Yanci
  • IAR da NAERLS Sun Shirya Taron Tattaunawa Da Masu Ruwa Da Tsaki Kan Noma Dawa A Najeriya