Kasashen Rasha Da Amurka Sun Kuduri Anniyar Kawo Karshen Yaki A Ukraine
Published: 19th, February 2025 GMT
Sakataren harkokin waje na kasar Amurka Marco Rubio ya bayyana cewa kasashen Amurka da Rasha sun kuduri anniyar kawo karshen yakin Ukrai, banda haka zasu kara kyautata dankon zumunci da tattalin arziki a tsakaninsu.
Shafin yanar gizo na labarai, Arabnews ta gwamnatin kasar Saudiya ya bayyana cewa, ya nakalto Rubio yana cewa kasashen biyu sun amince da sake bude ofisoshin jakadancin kasashen biyu a Washington da kuma Mosco, sannan zasu kafa kwamiti na musamman don kawo karshen yaki da kuma kyautata dangantaka tsakanin kasashen biyu.
Daga karshen zasu yi aiki tare don bunkasa tattalin arzikin kasashen biyu. Har’ila taron da kasar Saudiya ta dauki bakwancinsa a jiya Talata ya sami halattar tokwaransa na kasar Rasha Sergey Lavrov, kuma shi ne mataki na farko na hanyar kyautata dangantaka tsakanin kasashen biyu.
A taron na jiya dai babu wakilin kasar Ukraine, wacce da alamun ta kasa samun nasara a yakin da ta shiga da Rasha kimani shekaru 3 da suka gabata.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
A Kasar Gabon Brice Oligui Nguema Ya Lashe Zaben Shugaban Kasa
Shugaban gwamnatin rikon kwarya na kasar Gabon wanda ya tsaya takarar shugabancin kasar, ya lashe zabe da kawo 90.35% kamar yadda sanarwar ma’aikatar cikin gida ta sanar.
Brice Nguema ne dai ya jagoranci juyin mulkin da ya kifar da gwamnatin Ali Bango a watan Ogusta na shekarar 2023, ya kuma shiga cikin ‘yan takarar shugabancin kasar a wannan zaben.
Dan takara na biyu da yake binsa a baya, shi ne Alain Claude Bilie Bie Nze da ya sami kaso 3.02% na jumillar kuri’un da aka kada.
An sami halartar kaso 70.4% na jumillar wadanda su ka cancanci kada kuri’a da ya zama mai muhimmanci da zai kawo karshen mulkin rikon kwarya na soja.
Zaben na wannan lokacin shi ne irinsa na farko tun 2023.
Yawan masu kada kuri’ar dai sun kai 920,000, sai kuma masu sa idanu daga kasashen waje da sun kai 28,000.
Adadin mutanen kasar Gabon ya kai miliyan 2.3 da mafi yawancinsu suke rayuwar talauci duk da cewa Allah ya huwace wa kasar arzikin man fetur.
Masu Sanya idanu akan zaben sun ce, a kalla san sami kula da dukkanin ka’idojin zabe a cikin kaso 94.8 na mazabun kasar, kuma an baje komai a faifai ba tare da kumbaya-kumbiya ba da kaso 98.6%. Gabanin yin juyin mulkin da ya kawo karshen mulkin iyalan Bango na shekaru 50, Oligui Nguema ya kasance shugaban rundunar da take tsaron fadar shugaban kasa na kusan shekaru biyu.