USAID: Amurka za ta yi bincike kan ɗaukar nauyin Boko Haram
Published: 19th, February 2025 GMT
Gwamnatin Amurka ta ƙudiri aniyar gudanar da bincike kan yadda gwamnatocin da suka gabata suka riƙa sarrafa kuɗaɗen da aka fitar domin bai wa Nijeriya da wasu ƙasashen tallafi.
Hakan dai ya biyo bayan matakin da Shugaban Amurkan, Donald Trump ya ɗauka a watan Janairu na dakatar da duk wani tallafi da Amurkan ke bayarwa a ƙetare har na tsawon kwanaki 90.
Shugaba Trump ya bayyana cewa gwamnatinsa za ta gudanar da binciken ne a dalilin ruɗanin da ya dabaibaye duniya wanda ke cin karo da muradun Amurkan.
Haka kuma, Shugaba Trump ya ce za a gudanar da binciken ne domin amsa kiraye-kirayen ke yi wajen bitar ayyukan da Hukumar Bayar da Agaji ta USAID.
A bayan nan ne wani ɗan Majalisar Dokokin Amurka, Scott Perry, ya bayyana cewa hukumar raya kasashe ta Amurka (USAID) ke samar da kuɗaɗe ga kungiyoyin ’yan ta’adda, ciki har da Boko Haram.
Perry ya yi wannan iƙirarin ne yayin zaman sauraron rahoton kwamitin majalisar a kan yadda hukumomin gwamnatin Amurka ke aiwatar da ayyuka da sarrafa kuɗaɗe a ranar Alhamis ta makon jiya.
Zaman mai taken “yaki da barna: Kawar Da Annobar Almundahana Da Zamba,” ya maida hankali ne a kan zargin barnatar da kudaden masu biyan haraji.
“Waye ke samun wani banagare na kudaden? ko wani a ɗakin nan ya kiyaye waɗannan sunaye? saboda kudadenku, dala miliyan 697 a duk shekara, baya ga aika ƙarin kuɗaɗe ga Madrasas da ISIS da Al-Qa’ida da Boko Haram da ISIS Khorasan da sansanonin horas da ‘yan ta’adda. Wadannan su ne abubuwan da take daukar nauyi,” kamar yadda Perry ya bayyana.
Shafin yanar gizon kwamitin ya bayyana cewar zai yi aiki tare da ma’aikatar bin diddigin ayyukan hukumomin gwamnatin Shugaba Trump domin magance barna, da dakile almundahana tare da gudanar da cikakken bincike a kan yadda aka zambaci masu biyan harajin Amurka.
Ƙungiyar Boko Haram, wacce aka sani da Jamā’at Ahl as-Sunnah lid-Da’wah wa’l-Jihād, ƙungiya ce ta ‘yan ta’adda da ta ayyana kanta a matsayin mai tayar da ƙayar baya yankin arewa maso gabashin Nijeriya, da kuma ƙasashen Chadi, Nijar, Kamaru da kuma Mali.
Ƙungiyar ta shafe sama da shekaru 15 tana tashe-tashen hankula a yankin Arewa maso Gabashin Nijeriya, inda ta kashe dubun-dubatar mutane, a hare-haren da take kai wa ’yan sanda, da sojoji da fararen hula.
Zan gabatar da ƙudiri… — NdumeA kwanan ne shi ma Sanata Ali Ndume mai wakiltar Borno ta Kudu ya buƙaci gwamnatin Nijeriya ta gaggauta gudanar da bincike kan iƙirarin da ɗan majalisar dokokin Amurka ya yi na cewa hukumar USAID da gwamnatin Trump ta rufe ta tallafa wa ƙungiyoyin ta’addanci da suka haɗa har da Boko Haram a ƙasar.
Ndume ya ce ba batu ba ne da ya kamata gwamnatin Nijeriya ta naɗe hannunta, la’akari da girman barnar Boko Haram a Jihar Borno.
Ya ce zai gabatar da ƙudiri kan binciken zargin ɗan majalisar dokokin na Amurka.
“In an tashi binciken za mu yi tambayoyi, saboda haka za mu bincika domin mu ’yan Nijeriya da abun ya shafa ya kamata mu sa ido don a san matakan da za a ɗauka, saboda ba ƙaramin ɓarna Boko Haram suka yi mana ba,” in ji Ndume.
BBC ya ruwaito Sanata Ndume yana zargin cewa USAID ba ta aiki tare da hukumomin da ya kamata ta yi aiki tare da su a Nijeriya, lamarin da ya ke dasa ayar tambaya.
“Ba sa bari jami’an tsaronmu su sanya ido kan abubuwan da suke yi ballantana su ba da shawara.”
An dai ƙirƙiri Hukumar USAID a shekarun 1960 domin taimaka wa ayyukan agaji a madadin gwamnatin Amurka a kowanne yanki na duniya.
Tana da ma’aikata dubu 10, wanda kashi biyu bisa uku na aiki a ƙetare. Tana da cibiyoyi a sama da ƙasashe 60, sannan tana ayyuka daban-daban a sauran ƙasashe.
Sai dai galibin ayyukanta wasu ƙungiyoyin take bai wa kuɗi su aiwatar, nata shi ne sa ido da tabbatar da cewa an kashe kuɗaɗen bisa tsari.
Ayyukanta na da dimbin yawa. Misali, USAID ba tallafin abinci kaɗai take bayarwa a ƙasashe masu fama da yunwa ba, tana kuma aiki wajen gane inda za a fuskanci fari, da kuma inda za a buƙaci agajin gaggawa na yiwuwar ƙarancin abinci a nan gaba.
Galibin kasafin kuɗin USAID ana kashe su ne a fannin lafiya, irin su rigakafin Polio a ƙasashen da cutar ke yaɗuwa da kuma taimakawa wajen daƙile yaduwar cututtuka da ake yi wa kallon annoba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Boko Haram gudanar da bincike a gudanar da
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Tarayya Ta Bai Wa Jihar Jigawa Kayayyakin Noma Na Sama Da Naira Biliyan 5
Gwamnatin tarayya ta ce ta bai wa gwamnatin jihar Jigawa tallafin kayayyakin noma na sama da naira biliyan 5 domin bunkasa noman abinci a fadin jihar.
Ministan noma da samar da abinci Sanata Abubakar Kyari ya bayyana haka a lokacin da yake jawabi a garin Dabi da ke karamar hukumar Ringim a bikin ranar manoman alkama ta bana.
Ya bayyana cewa, matakin na daga cikin kudirin gwamnatin tarayya na tallafawa jihar wajen bunkasa noma domin kasuwanci.
Sanata Kyari ya yi nuni da cewa, gwamnatin tarayya ta gamsu sosai da yadda gwamnatin jihar Jigawa da manoma suka yi, na rungumar ayyukan noman rani.
Ministan ya yaba da kokarin gwamnatin jihar Jigawa da manoma, bisa goyon bayan shirin gwamnatin tarayya na bunkasa noman alkama, ta hanyar samar da kayan amfanin gona da dabarun zamani.
A nasa jawabin, Gwamna Umar Namadi ya jaddada kudirin gwamnatin jihar na bullo da wasu tsare-tsare da za su samar da guraben ayyukan yi da wadata kasa da abinci.
A cewarsa, tuni ya sayo taraktoci 300, ingantattun irin shuka, da sauran kayayyakin aikin gona domin noman amfanin gona daban-daban a fadin kananan hukumomin jihar 27.
Tun da farko a jawabinsa na maraba kwamishinan noma da albarkatun kasa na jihar Alhaji Muttaqa Namadi ya bayyana cewa gwamnatin tarayya ta bayar da tan 3,500 na ingantaccen irin alkama, da injinan ban ruwa 10,000 domin tallafawa noman alkama a jihar.
Ministan da mukarrabansa da Gwamna Umar Namadi sun ziyarci gonakin alkama da dama a Yakasawa da Dabi a karamar hukumar Ringim.
Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, kayayyakin da gwamnatin tarayya ta bayar sun hada da injinan ban ruwa 10,000, da lita 10,000 ta maganin kwari, taki na ruwa da injinan feshi.
Wasu daga cikin manyan baki da suka halarci bikin sun hada da, Darakta Janar na Gidan Rediyon Tarayya FRCN, Dr Mohammed Bulama, da sarakuna da malaman addini, da wakilan kungiyar sarrafa fulawa ta kasa, da manoman alkama da wasu manyan jami’an gwamnati.
Usman Muhammad Zaria