HausaTv:
2025-03-24@12:12:16 GMT

 Rasha Ta Kakkabo Jiragen  Sama Marasa Matuki 9 Na Kasar Ukiraniya

Published: 19th, February 2025 GMT

Ma’aikatar tsaron Rasha ta sanar da cewa, ta kakkabo jiragen saman marasa matuki 9 da kasar Ukiraniya ta harba mata.

Sanawar ta ma’aikatar harkokin tsaron Rasha ta ci gaba da cewa; A daren jiya ne  aka kakkabo jiragen sama  marasa matuki 3 na kasar Ukiraniya da aka harba a kan yankin Biryansk, sai kuma wani jirgin saman guda daya akan sararin samaniyar Tatrastan.

Bugu da kari makaman saman na Rasha  sun kakkabo wasu jiragen sama marasa matuki guda 4 a sararin samaniyar “Bahrul-Aswad”, sai kuma jirgi guda daya a saman yankin Tula.

A gefe daya  a jiya ne aka bude wani kwarya-kwaryar taro a tsakanin kasashen Amurka da Rasha a kasar Saudiyya domin tattauna hanyoyin kawo karshen yakin Ukinraniya.

Sakataren harkokin waje na kasar Amurka Marco Rubio ya bayyana cewa kasashen Amurka da Rasha sun kuduri anniyar kawo karshen yakin Ukrai.

A taron na jiya dai babu wakilin kasar Ukraine, wacce da alamun ta kasa samun nasara a yakin da ta shiga da Rasha kimani shekaru 3 da suka gabata.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnati ta kama mutum 347 kan haƙar ma’adanai ba bisa ƙa’ida ba

Gwamnatin Tarayya ta kama mutum 347 da ake zargi da haƙar ma’adanai ba bisa ƙa’ida ba a sassa daban-daban na Najeriya, inda aka gurfanar 143 a kotu.

Kama mutanen ya biyo bayan kafa wata runduna a shekarar 2024 don daƙile ayyukan haƙar ma’adanai ba ƙa’ida ba.

Kotun ƙoli ta tabbatar da Anyanwu a matsayin sakataren PDP Kwankwaso ya yi Allah-wadai da ayyana dokar ta-ɓaci a Ribas

Ministan Ma’adanai, Dele Alake, ya ce gwamnati na ƙoƙarin tabbatar da an hukunta mutum 327 da ke gaban kotu.

“A wannan watan, Babbar Kotun Tarayya da ke Ilorin ta yanke wa wasu ‘yan kasashen waje guda biyu, Yang Chao da Wu Shan Chuan, hukuncin ɗaurin gidan yari kan haƙar ma’adanai ba bisa ƙa’ida ba.

“Muna jinjina wa EFCC saboda ƙoƙarinta na gurfanar da masu aikata laifin,” in ji Alake.

Ministan ya ƙara da cewa runduna da aka kafa ta ƙwato wuraren haƙar ma’adanai guda 98, kuma ta gano wasu haramtattun wurare guda 457.

Gwamnati na shirin faɗaɗa ayyukan rundunar zuwa wasu jihohi tare da amfani da fasaha kamar jiragen sama marasa matuƙa da sauran na’urori don sanya ido.

“Rundunar ta ƙwace wuraren da wasu suka mamaye sama da shekaru 10 ba bisa doka ba.

“Wannan zai taimaka wajen bunƙasa kuɗaɗen shiga daga ɓangaren ma’adanai,” in ji shi.

Ministan ya tabbatar da cewa gwamnati za ta ƙara yawan jami’an tsaro da kayan aiki domin daƙile ayyukan haƙar ma’adanai ba bisa ƙa’ida ba.

Ya gargaɗi duk masu aikata irin waɗannan laifuka da su daina, ko kuma su fuskanci hukunci.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Firaministan Kasar Sin Ya Gana Da Sanata Steve Daines
  • Al-Huthi Ya Ce Kawo Wani Jirgin Ruwa Mai Daukar Jiragen Saman Yaki Gazawa Ce Ga Amurka
  • Za’a Gudanar Taron Tattaunawa Tsakanin Rasha Ta Amurka A Karo Na Biyu 2 A Birnin Rayad na Kasar Saudiya
  • Jakadan Sin A Amurka: Mayar Da Karin Haraji Makami Kaikayi Ne Da Zai Koma Kan Mashekiya
  • Amurka ta sake kai hare-hare Yemen
  • EFCC Ta Cafke Mutum 21 Bisa Zarginsu Da Zambar Intanet A Bauchi
  • Kwana Daya Bayan Kwace Fadar Shugaban Kasa, Sojojin Sudan Sun Kwace Babban Bankin Kasar
  • Gwamnati ta kama mutum 347 kan haƙar ma’adanai ba bisa ƙa’ida ba
  • Iran da UAE sun kirayi Isra’ila da Amurka da su kawo karshen hare-harensu a Gaza da Yemen
  • Saree: Filin jirgin saman Ben Gurion ba shi da aminci har sai an kawo karshen yakin Isra’ila a Gaza