Rundunar sojan kasar Sudan ta sanar da kwace iko da  hanyoyin da suke isa al-Fasha, kamar kuma yadda su ka killace fadar shugaban kasa dake birnin Khartum.

Sanarwar sojojin na Sudan ta kuma tabbatar da cewa, killace wannan hanyar da su ka yi, ya  yanke duk wata dama da dakarun “Rundunar Kai Daukin Gaggawa” suke da ita, ta samu dauki.

Birnin al-Fasha dai shi ne babbar birnin jahar Arewacin Darfur, kuma sojojin na Sudan sun ce, suna ci gaba da kutsawa a cikin jahar.

A gefe daya, wani jami’in sojan Sudan Yasir Adha, ya sanar da cewa; Babu yadda yaki zai tsaya har sai an ‘yanto da kowane taku daya na kasar Sudan daga hannun ‘yan tawaye.

Adha ya bayyana hakan ne dai a gaban sojoji a birnin Dabbah dake jahar Arewacin kasar.

A nashi gefen gwamnan jahar Darfur, Muna Minawi ya ce, sojojin na kasar Sudan suna ci gaba da ‘yanto da garuruwan kasar har zuwa birnin Janinah da shi ne babban birnin jahar Darfur ta yamma.

Haka nan kuma ya yi kira ga dukkanin masu goyon bayan “Rundunar Kai Daukin Gaggawa” a wannan yankin da su daina.

A cikin birnin Khartum kuwa sojojin Sudan sun katse duk wata hanyar kai musu dauki zuwa kusa da fadar shugaban kasa. A halin yanzu dai an killace “Dakarun Kai Daukin Gaggawa” dake cikin kusa da fadar ta shugaban kasa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kasar Iran Ya Mika Ta’aziyyar Ta Rasuwar Wanda Ya Assasa Hukumar  Makamashin Nukiliya Ta Iran

Shugaban kasar Iran Mas’ud Fizishkiyan ya bayyana alhininsa akan rasuwar Dr. Akbar I’itimadi wanda shi ne na farko da ya kafa hukumar makamashin Nukiliya ta Iran.

Wasikar ta’aziyyar da shugaban kasa ta kunsa ta ambaci cewa:  Shakka babu hidima mai kima da wannan masanin ya yi, ya share fagen gina da ci gaban fasahar makamashin Nukiliya a Iran da kuma mayar da kasar mai cin gashin kanta a wannan fage.

Har ila yau, shugaban kasar ta Iran ya mika sakon ta’aziyyarsa ga masana na Iran, da kuma iyalansa. Ya kuma yi addu’a da rokon Allah madaukin sarki da ya lullube shi da rahamarsa da kuma gafararsa, sannan ya bai wa iyalansa na hakuri.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Kasar Iran Ya Mika Ta’aziyyar Ta Rasuwar Wanda Ya Assasa Hukumar  Makamashin Nukiliya Ta Iran
  • A Kasar Gabon Brice Oligui Nguema Ya Lashe Zaben Shugaban Kasa
  • Sojojin Yemen Sun Kakkabo Jirgin Yakin Amurka Wanda Ake Sarrafa Shi Daga Nesa Na 19
  • Iran Ta Ce Za’a Gudanar Da Zagaye Na Gaba Tsakaninta Da Amurka Ne A Birnin Roma Na Kasar Italiya
  • Amnesty Ta Zargi  Rundunar “RSF” Ta Sudan Da Cin Zarafin Mata
  • Gaza: Sojojin HKI Sun Sake Kai Wa Asibitin “Ma’amadani Hari
  • Shugaban Burkina Faso Ya Yi Fatali Da Tayin Saudiyya Na Gina Masallatai 200 A Kasarsa
  • Jama’ar Gabon sun kada kuri’a a zaben shugaban kasa, na farko bayan mulkin zuri’ar Bongo
  • Isra’ila ta yi barazanar fadada hare-hare Gaza yayin da ta yanke Rafah daga birnin Khan Yunis
  • Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro