HausaTv:
2025-03-24@12:07:40 GMT

IRGC Ta Sanar Da Rusa  Kungiyar “Yan Leken Asirin Amurka Da HKI A Iran

Published: 19th, February 2025 GMT

Dakarun kare juyin juya halin musulunci na Iran sun sanar da gano da kuma rusa wata kungugun masu yi wa Amurka da Isra’ila leken asiri a yankin Arewacin Iran.

Kwamandan dakarun kare juyin juya halin musulunci a yankin Mazandaran dake arewacin Iran ne ya sanar da bankado da kuma rusa gungun masu yi wa abokan gabar leken asiri, ta hanyar amfani da ‘yan kasashen waje da masu zuwa yawon bude ido.

Kwamandan dakarun kare juyin juya halin na Mazandaran ya kara da cewa; Da dama daga cikin wadanda suke leken asirin suna fakewa ne a karkashin kamfanoni na kasuwanci, cibiyoyin al’adu da kuma kungiyoyin agaji.

 Bugu da kari kwamandan na dakarun kare juyin juya halin musulunci a gundumar ta Mazandaran ya kuma ce, bayan sa ido na jami’an leken asiri, dakarun na IRGC, sun yi nasarar gano su, da kuma rusa shekarsu ta leken asiri.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: dakarun kare juyin juya halin

এছাড়াও পড়ুন:

Babban Kusa A Kungiyar Hamas Salah Al-Bardawil Ya Yi Shahada

Kungiyar gwagwarmayar Falastinawa ta Hamas ta fitar da wata sanarwa dangane da shahadar Salah al-Bardawil, mamba a ofishin siyasa na kungiyar kuma wakilin majalisar dokokin Falasdinu.

A rahoton tashar Al-Alam, bayanin Hamas yana cewa: Dr. Salah Al-Bardawil, wanda ya yi fice a fagen siyasa, kafofin watsa labarai, da fagage na kasa da kasa, kuma ake kallonsa a matsayin daya daga cikin manyan kusoshin Hamas, wanda yake a kan gaba wajen gwagwarmaya da  sadaukarwa, ya yi shahada a kan tafarkin gaskiya.

Bayanin ya ci gaba da cewa: Bai taba gazawa wajen gudanar da ayyukansa na jihadi da hidima ga al’ummar Palastinu ba, ya kuma ci gaba da yin gwagwarmaya kan turba ta gaskiya da neman ‘yanci har zuwa karshen rayuwarsa.

Hamas ta jaddada cewa,  jinin Dakta Al-Bardawil da matarsa ​​da sauran shahidai wata fitila ce da za ta haskaka hanyar samun ‘yanci ga al’ummar Falastinu, kuma laifuffukan makiya ba za su taba raunana azama da jajircewar ‘yan gwagwarmaya a Falastinu ba.

A karshen wannan sanarwa da ta fitar a wannan Lahadi 23 ga Maris, 2025, kungiyar Hamas ta yi fatan samun rahama da aljannah ga Dr. Salah Bardawil da matarsa, tare da sauran wadanda suka yi shahada a kan tafarkin gaskiya.

Salah Al-Bardawil da matarsa ​​sun yi shahada ne a daren ranar 23 ga watan Ramadan, bayan wani hari da yahudawan sahyuniya suka kai a kan tantin su da suke a  yankin Al-Mawasi da ke yammacin birnin Khan Yunus.

Wannan harin dai wani bangare ne na kisan gilla da yahudawan Haramtacciyar Kasar Isra’ila  suke ci gaba da yi kan al’ummar Gaza marasa kariya, tare da samun cikakken goyon baya da karfin gwiwa da dukkanin taimako kan hakan daga gwamnatin kasar Amurka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ƴansandan Sun Gayyaci Sanata Karimi Kan Zargin Shigar Kungiyar Leƙen Asirin Rasha Majalisa’
  • Babban Kusa A Kungiyar Hamas Salah Al-Bardawil Ya Yi Shahada
  • Al-Huthi Ya Ce Kawo Wani Jirgin Ruwa Mai Daukar Jiragen Saman Yaki Gazawa Ce Ga Amurka
  • Amurka ta cire tukuicin wanda ya bayar da bayani kan mataimakin shugaban Taliban
  • Wakilin Sin Ya Yi Bayani Game Da Tunanin Sin Kan Kare Hakkin Dan Adam Da Kin Amincewa Da Siyasantar Da Hakkin Dan Adam
  •  Amurka: Turmp Yana Son Yin Yarjejeniya Ne Da Iran Ba Yaki Ba!
  • Sin Ta Ba Da Jawabi A Kwamitin Kare Hakkin Bil’adama Na MDD A Madadin Kungiyar Abokantaka Ta Inganta Hakkin Bil’adama
  • Iran da UAE sun kirayi Isra’ila da Amurka da su kawo karshen hare-harensu a Gaza da Yemen
  • Jagora: Amurka Ta Kwana Da Sanin Cewa Ba  Wata Riba Da Za Ta Ci Ta Hanyar Yi Wa  Iran Barazana
  • Gobara Ta Kashe Yaro A Sansanin ‘Yan Gudun Hijira A Maiduguri