HausaTv:
2025-04-14@18:19:35 GMT

IRGC Ta Sanar Da Rusa  Kungiyar “Yan Leken Asirin Amurka Da HKI A Iran

Published: 19th, February 2025 GMT

Dakarun kare juyin juya halin musulunci na Iran sun sanar da gano da kuma rusa wata kungugun masu yi wa Amurka da Isra’ila leken asiri a yankin Arewacin Iran.

Kwamandan dakarun kare juyin juya halin musulunci a yankin Mazandaran dake arewacin Iran ne ya sanar da bankado da kuma rusa gungun masu yi wa abokan gabar leken asiri, ta hanyar amfani da ‘yan kasashen waje da masu zuwa yawon bude ido.

Kwamandan dakarun kare juyin juya halin na Mazandaran ya kara da cewa; Da dama daga cikin wadanda suke leken asirin suna fakewa ne a karkashin kamfanoni na kasuwanci, cibiyoyin al’adu da kuma kungiyoyin agaji.

 Bugu da kari kwamandan na dakarun kare juyin juya halin musulunci a gundumar ta Mazandaran ya kuma ce, bayan sa ido na jami’an leken asiri, dakarun na IRGC, sun yi nasarar gano su, da kuma rusa shekarsu ta leken asiri.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: dakarun kare juyin juya halin

এছাড়াও পড়ুন:

Mutum ɗaya ya mutu a faɗan ƙungiyar asiri a Maiduguri

Wani matashi ɗan shekara 18 mai suna Bakura Muhammed, ya gamu da ajalinsa a wani rikici da ya ɓarke tsakanin ƙungiyoyin matasa masu gaba da juna da ake wa laƙabi da Malians a Maiduguri.

Majiyoyin leken asiri sun shaida wa Zaga-zola Makama cewa, rikicin ya faru ne da misalin karfe 4:30 na yammacin ranar 4 ga watan Afrilun nan a yankin Ajari da Tashar Lara, inda matasan ɓangarorin biyu suka yi artabu da juna.

An daɓa wa wanda aka kashen wuƙa a ciki, wanda ba tare da ɓata lokaci ba jami’an tsaro na Maidugurin suka ɗauke shi zuwa Asibitin Koyarwa na Jami’ar Maiduguri, inda jami’an lafiya suka tabbatar da rasuwarsa.

Wata majiyar ‘yan sanda ta ce, an kama wasu mutane bakwai masu shekaru tsakanin 15 zuwa 24.

Majiyar ta bayyana sunayen ababen zargin da aka kama da suka haɗa da Ba’abba Kyari mai kimanin shekara 20 sai Ali Alhaji Goni Ali dan shekara 20 da Muhammed Audu mai kimanin shekara 18, sai Ali Isa mai shekara 15 da Adam Sabir mai shekara 15 da Mohammed Tujja shekaru 17 da Usman Kasim dan shekara 24

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Tsoffin Ma’aikatan Hukumar Leken Asiri HKI  Mosad Sun Shiga Cikin Masu Kiran A Kawo Karshen Yaki Da Gaza
  • Hukumar OCHA Ta Bayyana Cewa Yahudawan Sahyoniyya Sun Ninninka Ayyukan Korar Falasdinawa A Yamma Da Kogin Jordan
  • Kasashen Larabawa Na Yankin Tekun Farisa Sun Yi Fatan Al-Khairi Ga Iran Da Amurka A Tattaunawar Shirin Nukliyar Kasar
  • Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Dakatar Da Matakin Kare-Karen Harajin Fito Kan Hajojin Da Ake Shigarwa Kasar
  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci: Makiya Suna Hasadan Ci Gaban Kasar Iran
  • Iran Zata Yaye Labulen Ire-Iren Makamanta Na Musamman Da Ta Mallaka Domin Kare Kai
  • Jiragen Yakin Kasar Amurka Suna Rusa Cibiyoyin Ilmi A Hare-Haren Da Suke Kaiwa Kasar Yemen
  • Mutum ɗaya ya mutu a faɗan ƙungiyar asiri a Maiduguri
  •  Limamin Tehran: Iran Ba Ta Tsoron Tattaunawa
  • MDD: Mafi Yawancin Wadanda Yaki Ya Ci A Gaza Mata Ne Da Kananan Yara