Hamas: Za A Mika Gawawwakin ‘Yan Mamaya Da Kuma Fursunoni Rayayyu A Ranakun Alhamis Da Asabar
Published: 19th, February 2025 GMT
Shugaban kungiyar Hamas Khalilul-Hayyah, ya fadi cewa; A ranakun Alhamis da Asabar masu zuwa ne za a mikawa ‘yan mamaya fursunoni rayayyu da kuma wasu gawawwaki a cikin bude wani shafin na musaya.
A jiya Talata ne dai Khalilul-Hayyah ya sanar da cewa, a bisa yadda aka cimma matsaya a musayar farko da aka yi, a cikin mako na shida daga kulla yarjejeniya, za a shiga wani sabon shafin na gaba na musayar fursunoni.
Khalil Hayya ya kuma ce a ranar Asabar din mai zuwa ne za a mika sauran fursunoni rayayyu da su ka saura, kamar yadda aka cimma matsaya da adadinsu shi ne 6, biyu daga cikinsu ana rike da su ne tun 2014, yayin da ‘yan mamaya za su saki sauran fursunonin da suke rike da su.
Shugaban na kungiyar Hamas ya bayyana hakan da cewa, yana nuni da yadda kungiyar take aiki da yarjejeniya, tare da yin kira da a tilasta HKI ta yi aiki da sharuddan yarjejeniyar ba tare da jan kafa ba. Haka nan kuma ya bayyana cewa kungiyar ta Hamas tana cikin shirin ko-ta –kwana na shiga shafi na gaba wanda shi ne dakatar da yaki da kuma janyewar sojojin mamayar daga Gaza.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Ko Raunin ‘Yan Wasa Zai Rage Wa Barcelona Karsashi A Kakar Bana?
Gwaje-gwajen da aka yi a ranar 17 ga Maris sun nuna cewa dan wasan tawagar farko Marc Casadó yana da rauni a gefen damansa, za a kara yin gwajin dan wasan don sanin girman raunin da kuma kwanakin da zai shafe ta na jinya, hakazalika Gwaje-gwaje a wannan rana kuma sun tabbatar da cewa dan wasan bayan kungiyar Iñigo Martinez yana da kumburi a gwiwarsa ta dama, za a yi wa dan wasan magani a Barcelona karkashin kulawar ma’aikatan lafiya na kungiyar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp