Shugaban kungiyar Hamas Khalilul-Hayyah, ya fadi cewa; A ranakun Alhamis da Asabar masu zuwa ne za a mikawa ‘yan mamaya fursunoni rayayyu da kuma wasu gawawwaki a cikin bude wani shafin na musaya.

 A jiya Talata ne dai Khalilul-Hayyah ya sanar da cewa, a bisa yadda aka cimma matsaya a musayar farko da aka yi, a cikin mako na shida daga kulla yarjejeniya, za a shiga wani sabon shafin na  gaba na musayar fursunoni.

 Khalil Hayya ya kuma ce a ranar Asabar din mai zuwa ne za a mika sauran fursunoni rayayyu da su ka saura, kamar yadda aka cimma matsaya da adadinsu shi ne 6, biyu daga cikinsu ana rike da su ne tun 2014, yayin da ‘yan mamaya za su saki sauran fursunonin da suke rike da su.

Shugaban na kungiyar Hamas ya bayyana hakan da cewa, yana nuni da yadda kungiyar take aiki da yarjejeniya, tare da yin kira da a tilasta HKI ta yi aiki da sharuddan yarjejeniyar ba tare da jan kafa ba. Haka nan kuma ya bayyana cewa kungiyar ta Hamas tana cikin shirin ko-ta –kwana na shiga shafi na gaba wanda shi ne dakatar da yaki da kuma janyewar sojojin mamayar daga Gaza.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Jagora Ya Gana Da Shuwagabannin Kungiyar Jihadul Islami A Nan Tehran

Jagoran juyin juya halin Musulunci A nan Iran Imam Sayyid Aliyul Khaminae ya gana da shuwagabannin kungiyar Jihadul Islami na kasar Falasdinu da aka mamaye a jiya Talata.

Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ya bayyana cewa Ziyad Nakhalah shugaban kungiyar ne ya jagoranci tawagar kungiyar zuwa ganawa da jagoran.

Labarin ya nakalto Jagoran juyin juya halin musulunci ya fadar cewa a halin yanzu babu wani abunda HKI zata yi a gaza sai idan kungiyoyi masu gwagwarmaya suna sun abin ya faru, saboda kekkyawar riko da suka yiwa yankin.

Imam Seyyed Ali Khamenei, ya yabawa kungiyoyin falasdinawa kan hadin kai da suka nuna a yankin da ya gabata.

Ziyad al-Nakhalah, babban sakataren kungiyar Jihad Islami,   ya bayyana cewa sun zo gaban Rahbar ne don tattauna mataki nag aba da yakamata su dauka a halin da ake ciki a kasar Falasdinu da aka mamaye.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Yi Tir Da Shugaban Hukumar IAEA Saboda Sanya Siyasa Da Daukan Bangare A Jawansa Na Baya Bayan Nan
  • Jami’an Diblomasiyya Daga Kungiyar G20 Da Dama Sun Isa Afrika Ta Kudu
  • Hamas Ta Mika Gawawwakin ‘Yan Isra’ila Hudu Ga Kungiyar Red Cross
  • Hamas Za Ta Saki Dukkan Fursunonin Isra’ila Da Ke Hannunta
  • Kungiyar Hamas Ta Yi Watsi Da Karin Shuruddan Gwamnatin ‘Yan Sayoniyya Kan Tsagaita Bude Wuta
  • Kissoshin Rayuwa. Sirar Imam Alhassan (a) 19
  • Jagora Ya Gana Da Shuwagabannin Kungiyar Jihadul Islami A Nan Tehran
  • Jaridar Maariv Ta Isra’ila Ta Bayyana Wasu Daga Cikin Hasarorin Da Yakin Gaza Ya Janyo Wa Gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya
  • Daga Munich Zuwa Addis Ababa, Ci Gaban Kasashe Daban Daban Na Tabbata