’Yan bindiga sun Kashe mutum 2 kan jinkirin biyan kuɗin fansa
Published: 19th, February 2025 GMT
’Yan bindiga sun kashe wasu mazauna ƙauyen Gwargwada da ke Ƙaramar Hukumar Kuje a saboda jinkirin biya musu kuɗin fansa.
Mutanen da aka kashe, sun haɗa da Mohammed Danladi da Nasiru Yusuf, wanɗanda aka sace su ne a ranar Laraba tare da wani makiyayi da wata mata a mahaɗar Gwombe, a kan hanyar Gwargwada zuwa Rubochi.
Wani ɗan uwan mamatan, Shuaibu Abdullahi, ya shaida wa Aminiya cewa maharan sun nemi iyalan waɗanda lamarin ya shafa su biya wa kowa Naira 500,000 amma Naira 500,000 suka iya tattaraws baki ɗayansu.
“Shugaban maharan ya kira mu ranar Juma’a, muka sanar da shi cewa Naira 500,000 kacal muka samu. Ba mu san cewa tuni sun kashe su ba saboda jinkirin biyan kuɗin fansar ba,” in ji shi.
Abdullahi ya ce bayan haka, ’yan bindigar sun saki makiyayin da matar da suka sace bayan an biya su Naira miliyan uku a maɓoyarsu da ke cikin dajin Kotonkarfe, a Jihar Kogi.
Shugaban yankin Gwargwada, Ugbada Alhaji Hussaini Agabi Mam, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce an sace matasan ne a hanyarsu ta dawowa daga Rubochi.
“Abin takaici, an kashe matasan nan biyu saboda kawai danginsu sun yi jinkiri wajen biyan kuɗin fansa,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa ba a samu gawarwakin mamatan ba domin an kai su cikin dajin Kotonkarfe.
“Na samu labarin cewa shugaban Ƙaramar Hukumar Kotonkarfe ya tura maharba da jami’an tsaro don su shiga dajin su nemo gawarwakin, amma har yanzu ba su same su ba,” in ji shi.
Rundunar ’Yan Sandan Babban Birnin Tarayya, ba ta fitar da wata sanarwa kan lamarin ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Birnin tarayya
এছাড়াও পড়ুন:
Za a binciki INEC kan jinkirin gudanar da zaɓen cike giɓi
Majalisar Wakilai ta umarci kwamitinta kan harkokin zaɓe da ya binciki Hukumar Zaɓe ta Ƙasa INEC dangane da jinkirin da take yi na gudanar da zaɓen cike giɓin wasu kujerun ’yan majalisar tarayya da na jihohi.
Majalisar a wannan Talatar ta kuma bayyana cewa jazaman ne kwamitin ya gayyaci Hukumar INEC domin ta bayar da dalilai kan tsaikon da aka samu da kuma yadda take ƙoƙarin yi wa tufkar hanci.
Gubar harsashi ta jikkata mutane dama a Zamfara Da wahala City ta yi nasara a gidan Madrid — GuardiolaAminiya ta ruwaito cewa Majalisar ta buƙaci kwamitin ya sauke wannan nauyi tare da miƙa mata rahoton bincikensa nan da makonni huɗu.
Wannan dai na zuwa ne bayan ƙorafin da wani ɗan majalisar, Jafaru Leko ya gabatar yana mai kafa hujja da Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya wanda ya ɗora wa INEC alhakin gudanar da zaɓe a faɗin ƙasar.
Kazalika, ya naƙalto sassa na 47 da 90 da ke cikin Kundin Tsarin Mulkin wanda ya hukunta assasa majalisun tarayya da na jihohi a matsayin wani rukuni na ’yancin ’yan ƙasa su samu wakilci.
Ya yi ƙorafin cewa tun bayan Zaɓen 2023 da waɗanda suka biyo baya, an samu giɓi a majalisun tarayya da na jihohi saboda wasu dalilai kamar mutuwa, karɓar wasu muƙaman ko ajiye aiki.
Jafara Leko ya ci gaba da ƙorafin cewa Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya ya yi tanadin gudanar da zaɓen cike giɓi cikin tsawon lokacin da bai gaza wata guda ba da samun giɓin.
Ya ƙara da cewa, gudanar da zaɓen wanda alhakinsa ya rataya a wuyan Hukumar INEC shi ne zai tabbatar da wakilcin kowace mazaɓa a ƙasar.
A cewarsa, wannan jinkiri da INEC take ci gaba da yi rashin biyayya ne ga Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya, lamarin da ke cutar da al’umma ko mazaɓar da ba su wakilci a hukumance.
Aminiya ta ruwaito cewa, a halin yanzu akwai kujerun ’yan Majalisar Tarayya bakwai masu giɓi da suka haɗa da na Majalisar Wakilai biyar da kuma biyu a Majalisar Dattawa.
Kujerun da ke da giɓi a Majalisar Wakilan sun haɗa da na jihohin Edo, Oyo, Kaduna, Ogun da Jigawa sai kuma na Majalisar Dattawa da suka ƙunshi Edo da Anambra.