’Yan bindiga sun Kashe mutum 2 kan jinkirin biyan kuɗin fansa
Published: 19th, February 2025 GMT
’Yan bindiga sun kashe wasu mazauna ƙauyen Gwargwada da ke Ƙaramar Hukumar Kuje a saboda jinkirin biya musu kuɗin fansa.
Mutanen da aka kashe, sun haɗa da Mohammed Danladi da Nasiru Yusuf, wanɗanda aka sace su ne a ranar Laraba tare da wani makiyayi da wata mata a mahaɗar Gwombe, a kan hanyar Gwargwada zuwa Rubochi.
Wani ɗan uwan mamatan, Shuaibu Abdullahi, ya shaida wa Aminiya cewa maharan sun nemi iyalan waɗanda lamarin ya shafa su biya wa kowa Naira 500,000 amma Naira 500,000 suka iya tattaraws baki ɗayansu.
“Shugaban maharan ya kira mu ranar Juma’a, muka sanar da shi cewa Naira 500,000 kacal muka samu. Ba mu san cewa tuni sun kashe su ba saboda jinkirin biyan kuɗin fansar ba,” in ji shi.
Abdullahi ya ce bayan haka, ’yan bindigar sun saki makiyayin da matar da suka sace bayan an biya su Naira miliyan uku a maɓoyarsu da ke cikin dajin Kotonkarfe, a Jihar Kogi.
Shugaban yankin Gwargwada, Ugbada Alhaji Hussaini Agabi Mam, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce an sace matasan ne a hanyarsu ta dawowa daga Rubochi.
“Abin takaici, an kashe matasan nan biyu saboda kawai danginsu sun yi jinkiri wajen biyan kuɗin fansa,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa ba a samu gawarwakin mamatan ba domin an kai su cikin dajin Kotonkarfe.
“Na samu labarin cewa shugaban Ƙaramar Hukumar Kotonkarfe ya tura maharba da jami’an tsaro don su shiga dajin su nemo gawarwakin, amma har yanzu ba su same su ba,” in ji shi.
Rundunar ’Yan Sandan Babban Birnin Tarayya, ba ta fitar da wata sanarwa kan lamarin ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Birnin tarayya
এছাড়াও পড়ুন:
Matasa sun kashe yaron da suka yi garkuwa da shi a Bauchi
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Bauchi, ta kama wasu matasa huɗu da ake zargi da yin garkuwa da kuma kashe wani yaro ɗan shekara shida, Shuaibu Safiyanu, a ƙauyen Sade da ke Ƙaramar Hukumar Darazo.
Aminiya ta ruwaito cewar mahaifin yaron, Safiyanu Abdullahi ne, ya sanar da Sarkin garinsu, Musa Isah, cewa a ranar 20 ga watan Maris, 2025, ɗansa ya ɓace.
Ɗan sa-kai ya kashe matasa biyu a Borno Gwamnatin Jigawa ta ƙaddamar da shirin noman rani na LallashiWashegari, wani ya kira shi a waya yana neman kuɗin fansa.
Da farko, ya nemi miliyan uku (₦3,000,000), amma daga baya suka rage zuwa Naira dubu ɗari biyu (₦200,000).
A ranar 21 ga watan Maris, aka gano gawar yaron a cikin daji, an ɗaure masa wuya da igiya.
Nan take aka kai shi asibiti, inda likitoci suka tabbatar da mutuwarsa.
Daga nan aka bai wa iyalansa gawarsa domin yi masa jana’iza.
Kakakin ’yan sandan Jihar, CSP Ahmed Mohammed Wakil, ya ce bayan samun rahoton lamarin, jami’an su suka fara bincike.
Sun fara binciken ne daga wajen POS da ke kusa da inda aka buƙaci a biya kuɗin fansar.
A yayin binciken, sun kama wani matashi mai shekara 23, Rabi’u Muhammadu daga ƙauyen Leka.
An gano cewa lambar wayarsa ce aka yi amfani da ita wajen kiran mahaifin yaron.
Sannan ’yan sanda sun gano asusun bankin da aka bayar don biyan kuɗin fansar: Lambar asusu: 0145285130 Sunan mai asusu: Ozochikelu Samson Banki: Union Bank PLC
Bayan kama Rabi’u, ya bayyana cewa Samson Ozochikel, mai shekara 35 daga ƙauyen Sade, shi ne ya shirya yadda za a sace yaron.
Ya kuma ambaci wasu matasa biyu, Muhammad Sani (Jingi), mai shekara 25, da Musa Usman (Kala), mai shekara 30, dukkaninsu daga ƙauyen Leka.
A halin yanzu, ’yan sanda suna tsare da su, kuma ana ci gaba da bincike a sashen binciken manyan laifuka (SCID).
Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar, ya tabbatar da cewa za su tabbatar da an yi adalci.
Ya kuma roƙi jama’a da su ci gaba da bai wa ’yan sanda haɗin kai, tare da sanar da su duk wani abun zargi ta layin kiran wayar gaggawa 112 ko Police Control Room a lamba 08156814656.
Rundunar ta jaddada ƙudirinta na kare rayuka da dukiyar al’ummar jihar.