Shugaba Tinubu, a wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Bayo Onanuga, ya fitar, ya yaba da irin hazakar da Ishiekwene ke da ita a fannin sharhi da nazari kan harkokin siyasa, tattalin arziki da halin da Nijeriya ke ciki.

 

Shugaban ya yaba da gudummawar da ya ke bayarwa wajen bunkasa yanayin kafafen yada labarai na Nijeriya, don haka, shugaba Tinubu na yi masa fatan alkairi a rayuwa ta gaba mai zuwa da karin kaifin basira.

 

Ya kuma roki Allah Madaukakin Sarki da Ya ba dan jaridan lafiya da samun biyan bukata a dukkan ayyukansa.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu Ya Kaddamar Da Ci Gaba Da Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 

Da yake jawabi a madadin shugaban kasa, Gwamna Uba Sani ya bayyana mahimmancin hanyar wadda ta hada babban birnin tarayya da jihohi sama da 12 dake fadin shiyyar Arewa ta tsakiya, Arewa maso Yamma, da Arewa maso Gabas.

 

A yayin taron da aka yi a Jere a karamar hukumar Kagarko a ranar Lahadin da ta gabata, Gwamna Sani ya bayyana cewa, an yi biris da aikin hanyar na tsawon shekaru da dama, wanda ya janyo asarar rayuka da kuma illa ga ci gaban tattalin arzikin yankin.

 

Sai dai Gwamnan ya kafa uzurin cewa, baya ga kudade, rashin tsaro da ake fama da shi a hanyar Kaduna zuwa Abuja a lokacin ne kamfanin Berger ya ki zuwa wurin domin ci gaba da aiki.

 

Amma a yanzu, hanyoyin da aka bi na magance matsalar tsaro yana haifar da sakamako mai kyau, domin masu ababen hawa na iya bin hanyar ba tare da fargabar an kai musu hari ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ci Gaba Da Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Tinubu ya kaddamar da aikin sake gyaran titin Abuja zuwa Kano
  • Xi Da Prabowo Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 75 Da Kulla Huldar Diplomasiyya Tsakanin Sin Da Indonesiya
  • Badaƙalar Miyagun Ƙwayoyi: Kotun Amurka ta ba da umarnin fitar da bayanai kan binciken Tinubu
  • Mutum ɗaya ya mutu a faɗan ƙungiyar asiri a Maiduguri
  • ‘Tell Your Papa’: NBC ta haramta amfani da waƙar da ke sukar Tinubu
  • Tsohon Kocin Super Eagles, Christian Chukwu, Ya Rasu Yana Da Shekaru 74
  • Saudiya Tace Shigo Da Agaji Cikin Gaza Bai Da Dangantaka Da Tsagaita Wuta
  • Abubuwa Da Yawa Na Faruwa Ba Tare Da Sanin Tinubu Ba – Tsohon Ma’aikacin Aso Rock
  • NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi