Aminiya:
2025-03-22@14:39:09 GMT

’Yan bindiga sun Kashe mutum 2, sun sace manoma 10 a Neja

Published: 19th, February 2025 GMT

’Yan bindiga sun kashe mutum biyu tare da yin awon gaba da aƙalla wasu 10 a hare-haren da suka kai Ƙananan Hukumomin Wushishi da Rafi a Jihar Neja.

Wani jami’in tsaro da ya nemi a sakaya sunansa ya shaida wa Aminiya cewa waɗanda aka kashe sun haɗa da ɗan sa-kai da wani mutum mai saran itace.

Hana Biza: Najeriya ta cancanci a girmama ta – Babban Hafsan Tsaro Rayuka 10 da dukiyar N11bn sun salwanta yayin zanga-zangar tsadar rayuwa a Kano

Har ila yau, ya ce wani ɗan sa-kai na daga cikin waɗanda aka sace.

“A halin yanzu, ’yan bindiga suna cikin dajin Akare. Sun sace ɗaya daga cikin ‘yan sa-kai, kuma yana da bindigogi biyu a tare da shi lokacin da suka yi awon gaba da shi.

“Ba mu san abin da za mu yi a yanzu ba. Mun shafe tsawon ranar ɗaya muna fafatawa da su. An kashe ɗaya daga cikin ’yan sa-kai da kuma wani mai saran itace,” in ji shi.

Mazauna yankin sun bayyana cewa har kawo hanzu ’yan bindigar suna cikin dajin tare da shanun da suka sace a yankin.

An ruwaito cewa sun kama mai saran itacen, tare da tilasta masa ya nuna musu hanya, sannan suka harbe shi.

Wasu majiyoyi sun bayyana cewa jami’an tsaro da ’yan sa-kai na ci gaba da ƙoƙarin bin sahun ‘yan bindigar.

Wani mazaunin yankin ya ce, “Mun ga ’yan bindigar suna tafiya da babura, uku-uku a kan kowanne.

“Suna wucewa ta wajen da suka saba bi a Kundu, a Ƙaramar Hukumar Rafi, sun nufin Ƙaramar Hukumar Mashegu tare da shanun da suka sace.”

Wani mazaunin Ƙaramar Hukumar Rafi, ya ce ’yan bindigar sun kuma kai hari wasu ƙauyuka a gundumar Gunna da safiyar ranar Laraba, inda suka ƙone rumbunan doya.

Da yake tabbatar da harin, Kwamishinan Tsaron Cikin Gida na Jihar Neja, Birgediya Janar Bello Abdullahi Mohammed (mai ritaya), ya ce, an tura ƙarin jami’an tsaro zuwa yankin.

“An riga an tura jami’an tsaro zuwa yankin, kuma suna bin sahun ’yan bindigar.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga hari yan bindigar

এছাড়াও পড়ুন:

Sojojin HKI Sun Kara Kisan Karin Falasdinawa 71 A Zirin Gaza

Rahotannin da suke fitowa daga yankin Gaza na kasar Falasdinu da aka mamaye sun nuna cewa, a cikin sa’o’ii 24 da suka gabata Falasdinawa 71 ne suka yi shahada a yayinda wasu da dama suka ji rauni.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa a wannan karon jiragen yakin HKI da jiragen ruwan yake daga tekun medeteranina sun cilla wuta kan garuruwan Beit –Lahia, Rafah da kuamKhan Yunus inda suka kashe da dama ko suka kaisu ga shahada.

Labarin ya kara da cewa sojojin yahudawan sun sake mamayar yankin Netzarim wanda ya raba arewa da kudancin zirin gaza a yau Alhamis.

Ya zuwa yanzu yawan falasdinawa da suka yi shahada ya kai 49,547 tun fara yakin Tufanul Aksa a ranar 7 ga watan Octoban shekara ta 2023, sannan yawan wadanda suka ji raunikuma ya karu zuwa 112,719 kamar yadda ma’aikatar lafiya ta zirin gaza ta bayyana.

HKI ta koma yaki bayan da ta yi watsi da tsagaita wuta da kungiyar Hamas, ita kadai a ranar Talanta da ta gabata.

A cikin kwanaki uku da suka gabata HKI ta kashe Falasdinawa kimani 500 a yankin Gaza. Inda kasha 2/3 daga cikinsu mata da yara ne.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Bam ya kashe mutum 4 da jikkata wasu a Borno
  • Sojoji sun ceto mutum 84 da ’yan bindiga suka sace a Katsina
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Shugaban Miyetti Allah A Filato
  • An wawushe motar abinci ta Hukumar WFP a Borno
  • Gobara ta ƙone gidaje tare da asarar dukiya a Gombe
  • Sojojin HKI Sun Kara Kisan Karin Falasdinawa 71 A Zirin Gaza
  • Mutane Fiye Da 30 Ne Suka Rasa Rayukansu A Lokacinda Motar Dawkar Gas Ta Yi Bindiga A Abuja Na Tarayyar Najeriya
  • Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 84, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 3 A Katsina
  • Sanƙarau ta kashe mutum 55 saboda rashin tsafta a Kebbi
  • ’Yan bindiga sun sace shugaban kasuwar kayan miya ta Akinyele a Oyo