Kungiyar Hamas Ta Yi Watsi Da Karin Shuruddan Gwamnatin ‘Yan Sayoniyya Kan Tsagaita Bude Wuta
Published: 19th, February 2025 GMT
Kungiyar Hamas ta ki amincewa da sabbin sharuddan fira ministyan gwamnatin mamayar Isra’ila na yarjejeniyar Gaza kashi na biyu
Fira ministan gwamnatin mamayar Isra’ila Benjamin Netanyahu a hukumance ya yanke shawarar fara tattaunawa kan mataki na biyu na yarjejeniyar Gaza, tare da sanya sabbin sharudda.
A yayin da ake fara shirye-shiryen fara gudanar da mataki na biyu na shawarwari tsakanin gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila da kungiyar Hamas bisa tsarin tsagaita bude wuta da yarjejeniyar musayar fursunoni, gwamnatin yahudawan sahayoniyya yana ci gaba da yin jinkiri ta hanyar kokarin kafa sabbin sharudda, yayin da kungiyar Hamas ta sanar da cewa, ba zata amince da ficewa daga zirin Gaza ko kuma kwance damarar makamanta ba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Amurka ta cire tukuicin wanda ya bayar da bayani kan mataimakin shugaban Taliban
Kungiyar Taliban ta ce Amurka ta cire tallafin dala miliyan 10 ga duk wanda ya bayar da bayanai kan Sirajuddin Haqqani, mataimakin shugaban kungiyar kuma ministan harkokin cikin gida.
A cewar Abdul Mateen Qani, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin cikin gidan Taliban, an janye tukuicin da aka bayar a baya a karkashin shirin bayar da lada na ma’aikatar harkokin wajen Amurka, tare da bayyana Haqqani a matsayin wanda ake nema ruwa a jallo.
Kawo yanzu dai babu wani martani daga ma’aikatar harkokin wajen Amurka dangane da matakin.
Haqqani shi ne shugaban kungiyar Haqqani, wata kungiya mai karfi a cikin kungiyar Taliban wacce ta shahara wajen ayyukanta da makamai.
Duk da ayyana shi a baya a matsayin “dan ta’adda na duniya” da Amurka ta yi, Haqqani ya rike babban matsayi a cikin gwamnatin Taliban, inda aka dora masa alhakin kula da tsaron cikin gida na Afghanistan.
Kasancewar sa a cikin gwamnatin ya kasance wani batu ne da ake ta takun saka tsakanin ‘yan Taliban da gwamnatocin kasashen yammacin duniya, wadanda ke ci gaba da kakaba takunkumi tare da kin amincewa da mulkin kungiyar a hukumance.
Zargin cire ladan ya zo ne a daidai lokacin da kungiyar Taliban ke kokarin ganin ta samu halacci a fagen kasa da kasa, a yayin da take kokarin kulla huldar diflomasiyya, da sakin kadarorin babban bankin Afganistan da Washington ta rike, da kuma rage takunkumin hana tafiye-tafiye a kan jami’ansu.