Kungiyar Hamas Ta Yi Watsi Da Karin Shuruddan Gwamnatin ‘Yan Sayoniyya Kan Tsagaita Bude Wuta
Published: 19th, February 2025 GMT
Kungiyar Hamas ta ki amincewa da sabbin sharuddan fira ministyan gwamnatin mamayar Isra’ila na yarjejeniyar Gaza kashi na biyu
Fira ministan gwamnatin mamayar Isra’ila Benjamin Netanyahu a hukumance ya yanke shawarar fara tattaunawa kan mataki na biyu na yarjejeniyar Gaza, tare da sanya sabbin sharudda.
A yayin da ake fara shirye-shiryen fara gudanar da mataki na biyu na shawarwari tsakanin gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila da kungiyar Hamas bisa tsarin tsagaita bude wuta da yarjejeniyar musayar fursunoni, gwamnatin yahudawan sahayoniyya yana ci gaba da yin jinkiri ta hanyar kokarin kafa sabbin sharudda, yayin da kungiyar Hamas ta sanar da cewa, ba zata amince da ficewa daga zirin Gaza ko kuma kwance damarar makamanta ba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Gombe ta horar da makiyaya kan sabbin hanyoyin kiwo
Gwamnatin Jihar Gombe ta horar da makiyaya 684, ciki har da nakasassu, mata, matasa, da tsofaffin ma’aikata, kan sabbin dabarun kiwon awaki da kasuwancinsu.
Wannan horo ya gudana ne ƙarƙashin shirin Livestock Productivity and Resilience Support (L-PRES).
Rigima ta sake kaurewa tsakanin PDP da APC a Zamfara Mutum 11 sun kuɓuta daga hannun Boko Haram a BornoKwamishinan Aikin Gona, Kiwo, da Hada-hadar Ƙungiyoyi na Jihar Gombe, Dokta Barnabas Malle ne, ya jagoranci ƙaddamar da horon a Gombe.
Yayin da yake jawabi, ya jaddada ƙudirin gwamnatin Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya, na inganta kiwon dabbobi da tallafa wa al’umma.
Ya ce: “Shirin ya dace da manufofin gwamnati na bai wa kowa damar cin gajiyar shirye-shiryen da ake gudanarwa.”
Shugaban shirin L-PRES na Gombe, Farfesa Usman Bello Abubakar, ya bayyana cewa horon zai taimaka wa makiyaya wajen ƙara ƙwarewa da haɓaka kiwon awaki.
Ya ce: “Mun mayar da hankali kan makiyaya saboda muhimmiyar rawar da suke takawa wajen samar da awaki a tsakanin al’ummarmu.
“Manufarmu ita ce ƙara musu ƙwarin gwiwa da ƙwarewa don su inganta rayuwarsu.”
Farfesa Abubakar, ya ƙara da cewa buƙatar naman awaki a duniya na ƙaruwa, don haka Gombe na da shirin kafa cibiyar kiwon awaki ta zamani da kuma babbar kasuwa ta yanka dabbobi a Najeriya.
A yayin horon, an koyar da mahalarta yadda ake:
Zabar nau’in awaki masu inganci Ciyarwa mai kyau Rigakafin cututtuka Inganta muhalli don kiwoDabarun kasuwanci da sarrafa kayayyakin da ake samu daga awaki
Shugaban Ƙungiyar Masu Nakasassu ta Jihar Gombe, Ja’o Sarkin Aiki, ya yaba wa gwamnatin bisa wannan horo
“Wannan horo zai taimaka mana wajen bunƙasa kiwonmu da kuma dogaro da kanmu don samun ingantacciyar rayuwa.”