Kungiyar Hamas ta ki amincewa da sabbin sharuddan fira ministyan gwamnatin mamayar Isra’ila na yarjejeniyar Gaza kashi na biyu

Fira ministan gwamnatin mamayar Isra’ila Benjamin Netanyahu a hukumance ya yanke shawarar fara tattaunawa kan mataki na biyu na yarjejeniyar Gaza, tare da sanya sabbin sharudda.

A nata bangaren kungiyar Hamas ta ki amincewa da sharadin ficewarta daga yankin Zirin Gaza da kuma yin fatali da bukatar ajiye makamai a matsayin wani bangare na kowace yarjejeniya.

A yayin da ake fara shirye-shiryen fara gudanar da mataki na biyu na shawarwari tsakanin gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila da kungiyar Hamas bisa tsarin tsagaita bude wuta da yarjejeniyar musayar fursunoni, gwamnatin yahudawan sahayoniyya yana ci gaba da yin jinkiri ta hanyar kokarin kafa sabbin sharudda, yayin da kungiyar Hamas ta sanar da cewa, ba zata amince da ficewa daga zirin Gaza ko kuma kwance damarar makamanta ba.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Gombe ta horar da makiyaya kan sabbin hanyoyin kiwo

Gwamnatin Jihar Gombe ta horar da makiyaya 684, ciki har da nakasassu, mata, matasa, da tsofaffin ma’aikata, kan sabbin dabarun kiwon awaki da kasuwancinsu.

Wannan horo ya gudana ne ƙarƙashin shirin Livestock Productivity and Resilience Support (L-PRES).

Rigima ta sake kaurewa tsakanin PDP da APC a Zamfara Mutum 11 sun kuɓuta daga hannun Boko Haram a Borno

Kwamishinan Aikin Gona, Kiwo, da Hada-hadar Ƙungiyoyi na Jihar Gombe, Dokta Barnabas Malle ne, ya jagoranci ƙaddamar da horon a Gombe.

Yayin da yake jawabi, ya jaddada ƙudirin gwamnatin Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya, na inganta kiwon dabbobi da tallafa wa al’umma.

Ya ce: “Shirin ya dace da manufofin gwamnati na bai wa kowa damar cin gajiyar shirye-shiryen da ake gudanarwa.”

Shugaban shirin L-PRES na Gombe, Farfesa Usman Bello Abubakar, ya bayyana cewa horon zai taimaka wa makiyaya wajen ƙara ƙwarewa da haɓaka kiwon awaki.

Ya ce: “Mun mayar da hankali kan makiyaya saboda muhimmiyar rawar da suke takawa wajen samar da awaki a tsakanin al’ummarmu.

“Manufarmu ita ce ƙara musu ƙwarin gwiwa da ƙwarewa don su inganta rayuwarsu.”

Farfesa Abubakar, ya ƙara da cewa buƙatar naman awaki a duniya na ƙaruwa, don haka Gombe na da shirin kafa cibiyar kiwon awaki ta zamani da kuma babbar kasuwa ta yanka dabbobi a Najeriya.

A yayin horon, an koyar da mahalarta yadda ake:

Zabar nau’in awaki masu inganci Ciyarwa mai kyau Rigakafin cututtuka Inganta muhalli don kiwo

Dabarun kasuwanci da sarrafa kayayyakin da ake samu daga awaki

Shugaban Ƙungiyar Masu Nakasassu ta Jihar Gombe, Ja’o Sarkin Aiki, ya yaba wa gwamnatin bisa wannan horo

“Wannan horo zai taimaka mana wajen bunƙasa kiwonmu da kuma dogaro da kanmu don samun ingantacciyar rayuwa.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hamas Ta Mika Gawawwakin ‘Yan Isra’ila Hudu Ga Kungiyar Red Cross
  • Hamas Za Ta Saki Dukkan Fursunonin Isra’ila Da Ke Hannunta
  • An Rantsar Da Sabbin Shugabannin Kungiyar Manyan Sakatarorin Jihar Zamfara
  • Gwamnatin Gombe ta horar da makiyaya kan sabbin hanyoyin kiwo
  • Hamas: Za A Mika Gawawwakin ‘Yan Mamaya Da Kuma Fursunoni Rayayyu A Ranakun Alhamis Da Asabar
  • Jagora Ya Gana Da Shuwagabannin Kungiyar Jihadul Islami A Nan Tehran
  • Gwamnatin Niger Ta Hana Yan Najeriya Dauke Da Passpor Ta Na ECOWAS Shiga Kasar
  • Shugaban Amurka Ya Ce: Sun Baiwa Fira Ministan Gwamnatin Isra’ila Damar Ya Aikata Abin Da Yake So
  • Jaridar Maariv Ta Isra’ila Ta Bayyana Wasu Daga Cikin Hasarorin Da Yakin Gaza Ya Janyo Wa Gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya