Shugaban Kasar Iran Ya Tattauna Da Sarkin Kasar Qatar Kan Muhimmancin Hadin Gwiwa Da Taimakekkeniya Tsakaninsu
Published: 19th, February 2025 GMT
Shugaban kasar Iran da Sarkin kasar Qatar sun jaddada muhimmancin hadin gwiwa da taimakekkeniya tsakanin kasashen yankin Gabas ta Tsakiya
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian da sarkin Qatar Sheikh Tamim bin Hamid Al Thani sun gudanar da taron manema labarai na hadin gwiwa a birnin Tehran, inda suka jaddada karfin dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu, da kuma muhimmancin kara inganta taimakekkeniya a tsakanin kasashensu.
Shugaban na Iran ya fada a yammacin yau Laraba cewa: Ci gaba da tarukan tsakanin jami’an kasashen biyu ke yi na tabbatar da kyakkyawar alakar da ke tsakaninsu, yana mai jaddada karfafa alaka da kasashe makwabta, musamman kasar Qatar, a matsayin wani muhimmin ka’ida na manufofin ketare na Iran.
Shugaban kasar ya ci gaba da cewa: Sun tattauna da Sarkin Qatar kan batutuwan da suka shafi kasashen biyu ta hanyar da za ta tabbatar da moriyar kasashensu, kuma an yanke wasu muhimman shawarwari na raya kasa da zurfafa dangantaka da bude sabbin hanyoyin hadin gwiwa. Sarkin Qatar ya kuma jaddada bukatar samar da sabbin damar gudanar da hadin gwiwa.
Shugaba Pezeshkian ya kara da cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta yi imanin cewa, kasashen yankin suna da karfin daukar matakai na tabbatar da zaman lafiya da tsaro a yankin, bisa tushen kyakkyawar makwabtaka da mutunta juna da kyautata mu’amala mai ma’ana, da share fagen kafa wani tsari na hadin gwiwa da taimakekkeniya.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Shugaban kasar hadin gwiwa
এছাড়াও পড়ুন:
Kasashen duniya da kungiyoyin kasa da kasa na fatan nasara ga tattaunawar Amurka da Iran
Kasashen duniya da kungiyoyin kasa da kasa na fatan nasara ga tattaunawar Iran da kuma Amurka.
Kasar Iraki ta bayyana fatan tattaunawar za ta aifar da kwanciyar hankali a yankin
Ministan harkokin wajen Iraki ya bayyana goyon bayansa ga tattaunawar tsakanin Iran da Amurka, yana mai bayyana fatan Bagadaza na ganin cewa hakan zai samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.
A wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen Iraki ta fitar ta ce “Hussein ya karbi bakuncin mataimakin ministan harkokin wajen Iran Saeed Khatibzadeh a ranar Juma’a a gidansa da ke birnin Antalya na Turkiyya.
Sanarwar ta kara da cewa “a yayin ganawar, an tattauna dangantakar da ke tsakanin kasashen dake makobtaka da juna da kuma hanyoyin karfafa su a fannoni daban-daban.”
“Hussein ya yi maraba da tattaunawar ta tsakanin Jamhuriyar Musulunci ta Iran da Amurka, yana mai bayyana fatansa na cewa a wannan shawarwarin za a samu sakamako mai kyau da zai taimaka wajen samun kwanciyar hankali a yankin.”
Shi ma babban daraktan hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA Rafael Grossi ya bayyana fatansa na ganin an cimma yarjejeniyar nukiliyar tsakanin Iran da Amurka cikin gaggawa.
Grossi ya ce yana da kwarin gwiwar cewa bangarorin biyu za su iya warware sabanin ra’ayi a fannin tattalin arziki da cinikayya ta hanyar yin shawarwari kafada-da-kafada da hadin gwiwa don cin moriyar juna.
Stephane Dujarric, mai magana da yawun babban sakataren MDD Antonio Guterres, ya bayyana fatansa game da tattaunawar ta tsakanin Amurka da kuma Iran.