Gidauniyar Tunawa Da Sir Ahmadu Bello Za Ta Gudanar Da Taronta Karo Na 11 A Bauchi.Gidauniyar Tunawa da Sir Ahmadu Bello ta sanar da cewa za ta gudanar da bikin tunawa da Sir Ahmadu Bello na shekara karo na 11 a ranar Litinin, 24 ga Fabrairu, 2025, a Bauchi, Jihar Bauchi.

Taron, wanda aka shirya tare da hadin gwiwar Gwamnatin Jihar Bauchi, zai girmama marigayi Sir Ahmadu Bello, Sardaunan Sakkwato kuma Firaministan tsohuwar Yankin Arewa.

A bana, taken laccar shi ne “Arzikin Halitta: Juya Albarkatun Yankin Arewa Zuwa Ci Gaban Tattalin Arziki Mai Dorewa.”

Tattaunawar za ta mayar da hankali ne kan yadda za a yi amfani da albarkatun noma da ma’adanai da ruwa don bunkasa ci gaban tattalin arzikin yankin.

Duba da kalubalen tattalin arzikin da Najeriya ke fuskanta, musamman yankin Arewa, laccar za ta bayyana rawar da gwamnati da ɓangarori masu zaman kansu da kungiyoyin al’umma za su taka wajen inganta sarrafa albarkatu da bunkasa darajar kayayyaki da samar da ayyukan yi.

Babbar lacca za a gabatar da ita ne daga bakin Dr. Mansur Mukhtar (Sarkin Bai Kano), tsohon Mataimakin Shugaban Bankin Musulunci kuma Shugaban Bankin Masana’antu na Najeriya.

Ana sa ran Sanata George Akume, Sakataren Gwamnatin Tarayya, zai kasance Babban Bako na Musamman a wurin taron.

Haka nan, ana sa ran halartar Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya na Jihar Gombe, wanda shi ne Shugaban Kungiyar Gwamnonin Arewa, kuma zai jagoranci taron.

Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Mohammed, zai kasance Babban Mai Masaukin baki. Haka kuma, ana sa ran halartar gwamnonin jihohi da ministoci da ‘yan majalisa da sarakuna da sauran manyan baki daga sassa daban-daban.

A cewar Darakta-Janar na Gidauniyar, Injiniya Dr Abubakar Gambo Umar, albarkatun yankin Arewa na da babban damar sauya tattalin arzikin yankin.

“Sai dai dole mu dauki matakan da za su tabbatar da sarrafa albarkatunmu cikin adalci da dorewa, domin amfanin kowa da kowa,” in ji shi.

A yayin taron, gidauniyar za ta bayar da tallafin karatu ga dalibai marasa galihu daga Jihar Bauchi da ke karatu a manyan makarantu domin tallafa musu.

Bugu da kari, za a karrama wasu fitattun mutane da lambar yabo saboda gudunmawar da suka bayar ga cigaban al’umma.

Har ila yau, za a gudanar da shirin ba da agajin lafiya domin samar da hidimar kiwon lafiya ga al’ummar yankin.

Gidauniyar Tunawa da Sir Ahmadu Bello an kafa ta ne domin ci gaba da girmama gadon shugabanci da ilimi da ci gaban tattalin arziki da marigayi Sardaunan Sakkwato ya assasa.

Bikin tunawa na kowace shekara, wanda ke gudana a jihohi 19 na Arewa, na zama wata kafa ta tattaunawa kan ci gaban yankin da shugabanci.

Gidauniyar ta nemi afuwar duk wani rashin jin dadi da sauya ranar taron ka iya haifarwa, tare da gode wa duk masu mara mata baya.

Rel: Khadija Kubau

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Gidauniyar Tunawa Da Sir Ahmadu Bello Za Ta Gudanar Karo Taronta Gidauniyar Tunawa da Sir Ahmadu Bello Gidauniyar Tunawa Da Sir Ahmadu Bello yankin Arewa Jihar Bauchi

এছাড়াও পড়ুন:

Rurum Ya Shawarci Mafarautan Arewa Da Su Daina Zuwa Kudu Farauta 

Ya bayyana cewa shiga wani yanki da ba a fahimtar yaren juna ɗauke da makamai na iya janyo fargaba da tashin hankali.

“Ka yi tunanin idan wasu daga Kudu sun shigo ƙauyanku ɗauke da makamai kuma ba ku fahimtar yaren juna — za ku ji tsoro. Haka nan idan mutanenmu suka shiga yankin Kudu da makamai, su ma za a ji tsoro,” in ji shi.

Rurum ya ce zai gana da shugabannin ƙungiyoyin masu farauta a jihar domin daƙile wannan ɗabi’a, ya kuma buƙace su da su nemo hanyar nema wa kansu asiri .

“Wasu su tafi farauta su dawo ba tare da sun kamo ko ɓeran daji ba. Bai dace su ci gaba da haka ba. Ya kamata mu nemi wata hanya ta zaman lafiya da kwanciyar hankali,” in ji shi.

Haka kuma, ya bayar da gudunmawar naira miliyan biyar ga iyalan waɗanda suka rasu, sannan ya sha alwashin gina makaranta a garin domin girmama su.

Rurum ya kuma ce zai haɗa kai da Sanata Kawu Sumaila domin su kai ƙudiri a majalisa a kan kisan da aka yi wa mafarautan jihar a garin Uromi don ganin an yi wa waɗanda abin ya shafa adalci.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwamitin Gudanar da Kasuwa Maras Shinge Ta Maigatari Sun Ziyarci Fadar Gumel
  • Ba a taɓa Dimokraɗiyya mai tsafta a Najeriya kamar mulkin Tinubu ba – Matawalle
  • Rurum Ya Shawarci Mafarautan Arewa Da Su Daina Zuwa Kudu Farauta 
  • An Fara Bada Horo Ga Masu Horas da Maniyatan Bana A Jigawa
  • An Fara Bada Horo Ga Masu Horas da Mabiyan Bana A Jigawa
  • Hukumar Alhazai ta Jigawa Ta Shirya Bitar Ga Malaman Bita na Kananan Hukumomi 27
  • Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Taron Ƙarawa Ma’aikatan Jinƙai Sani A Jihar Kano
  • An Gudanar Da Taron Kasa da Kasa Don Tallafawa Yan Gudun Hijirar A Sudan
  • Samarwa Matasa Abun Yi Shi Zai Kawo Ƙarshen Ta’addancin Boko Haram Da ‘Yan Bindiga – Zulum 
  • Hajj 2025: Hukumar Alhazai Ta Shirya Taron Bita Ga Mahajjata a Jihar Kwara