Kamfanonin Sin Masu Zaman Kansu Na Taka Rawar Gani Ga Bunkasuwar Tattalin Arzikin Duniya
Published: 20th, February 2025 GMT
Kafofin yada labarai da manazarta na kasa da kasa, sun jinjinawa babban taron ‘yan kasuwan kamfanonin kasar Sin masu zaman kansu da aka gudanar ranar Litinin, inda suka ce gwamnatin Sin na marawa wadannan kamfanonin baya wajen taka rawar gani a bangaren kimiyya da fasaha da kirkire-kirkire, kuma Sin ta gabatar da sako mai yakini na karawa wadannan kamfanoni kwarin gwiwar bunkasuwa.
A wannan taro dai, ba nanata niyyar nacewa ga manufofi masu tushe da ake bi wajen raya kamfanoni masu zaman kansu a nan kasar Sin kadai aka yi ba, an kuma gabatar da alkiblar samun ingantattun ci gaba yadda ya kamata a wannan bangare. Hakan ya sa, “kwarin gwiwa” ta sake zama muhimmiyar kalma ga kasashen waje don leka bunkasuwar kasar Sin.
A shekarar da ta gabata, yawan kudin shige da fice da wadannan kamfanoni suka mallaka ya karu daga kashi 43.% na 2019 zuwa kashi 55.5%, kuma cikin shekaru 6 a jere, sun zama bangare mafi girma a nan kasar Sin ta fuskar cinikin shige da fice. A matsayinsu na jigon cinikin shige da fice, kamfanonin Sin masu zaman kansu sun taka rawar gani a bangaren ba da tabbaci ga tsarin samar da kayayyaki a duniya. (Amina Xu)
এছাড়াও পড়ুন:
Gombe Za Ta Kashe Naira Biliyan 1.1 Don Samar Da Fitilun Hanya Masu Aiki Da Hasken Rana
Ya sanar cewa karamar hukumar ta kuduri aniyar daukar tsauraran matakai don dakile wannan barazana ta hanyar tura jami’an GOSTEC da Operation Hattara don inganta tsaro.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp