Aminiya:
2025-04-15@23:24:42 GMT

UCL: Real Madrid ta murƙushe Man City da ci 3

Published: 20th, February 2025 GMT

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Real Madrid ta sake doke Manchester City da ci 3 da 1 a filin wasa na Bernabeu.

Madrid ta karɓi baƙuncin Man City a wasan zagaye na biyu na gasar Zakarun Turai, bayan doke ta a gida da ci 3 da 2.

Gobara ta ƙone gidaje, dabobbi da kayan abinci a Kano Hana Biza: Najeriya ta cancanci a girmama ta – Babban Hafsan Tsaro

Kylian Mbappe ne ya zama tauraro a wannan wasan, inda ya jefa wa Manchester City ƙwallaye uku rigis a raga.

Ɗan wasan gaban na Real Madrid, ya fara jefa ƙwallo ta farko a minti na 4 da fara wasa, sannan ya jefa ƙwallo ta biyu a minti na 33.

Bayan dawowa daga hutun rabin lokaci ne, Mbappe ya sake jefa ƙwallo ta uku a ragar Manchester City a minti 61.

A minti na 92 ɗan wasan Manchester City, Nico Gonzalez, ya warware mata ƙwallo ɗaya.

A haka wasan ya ƙare, amma Jude Bellingham ya samu katin gargaɗi, wanda hakan ke nufin ba zai buga wa Madrid wasanta na gaba a gasar ba.

Idan aka raba jadawalin ƙungiyoyin da za su kara da juna, Real Madrid za ta iya haɗuwa da Bayer Leverkusen ko Atletico Madrid.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gasar Zakarun Turai

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Kano Za Ta Sake Buɗe Makarantun Kwana 10 Don Inganta Ilimin Yara Mata

Ta bayyana cewa gwamnatin jihar ta bayyana ayyana dokar ta-ɓaci a harkar ilimi, kuma ta kashe biliyoyin Naira wajen gyara da sabunta makarantun kwana, inda ta ce “nan ba da jimawa ba za a sake buɗe su don yara mata su ci gaba da samun ilimi.”

Ta kuma ƙara da cewa wasu daga cikin makarantun da ke aiki kamar WTC Kano da GGS Dala na karɓar yara daga yankunan da ke kewaye da su, kuma za a yi amfani da irin wannan tsari a sauran makarantun da za a sake buɗewa.

Hajiya Amina ta ƙara da cewa ofishinta ya samu amincewa daga ma’aikatar don gudanar da bincike a wasu yankuna da ke fama da yawan yara mata da ba sa zuwa makaranta ko kuma waɗanda suka daina karatu, don gano matsalolinsu da kawo mafita.

A nasa ɓangaren, Abdulaziz Musa, wanda shi ne mai kula da shirin “Bridging Access to Girls Education” na BCAI, ya bayyana cewa manufar taron ita ce tattauna ci gaba da ƙalubale da kuma amfani da kuɗaɗen da aka ware don ilimin ’yan mata tare da wakilan gwamnati, ƙungiyoyin fararen hula, da kuma ’yan jarida.

Ya ce duk da ci gaban da aka samu, har yanzu akwai ƙalubale mai yawa, don haka akwai buƙatar haɗin gwiwa tsakanin gwamnati da ƙungiyoyi masu zaman kansu domin ciyar da harkar gaba.

Ya ƙara da cewa sun samar da wani tsarin kasafin kuɗi da ya dace da buƙatun mata wanda gwamnati za ta iya amfani da shi wajen tsara yadda za a kashe kuɗin da aka ware don inganta ilimin yara mata a Jihar Kano.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Kano Za Ta Sake Buɗe Makarantun Kwana 10 Don Inganta Ilimin Yara Mata
  • Tinubu ya kaddamar da aikin sake gyaran titin Abuja zuwa Kano
  • An sake kama wasu mafarauta ’yan Kano a Jihar Edo
  • HKI Ta Jefa Boma-Bomai A Kan Asbiti Tilo Da Ya Rage Yake Aiki A Arewacin Gaza
  • Gaza: Sojojin HKI Sun Sake Kai Wa Asibitin “Ma’amadani Hari