Aminiya:
2025-04-14@17:42:17 GMT

Real Madrid ta fitar da Man City a Gasar Zakarun Turai

Published: 20th, February 2025 GMT

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Real Madrid ta sake doke Manchester City da ci 3 da 1 a filin wasa na Bernabeu.

Madrid ta karɓi baƙuncin Man City a wasan zagaye na biyu na gasar Zakarun Turai, bayan doke ta a gida da ci 3 da 2.

Gobara ta ƙone gidaje, dabobbi da kayan abinci a Kano Hana Biza: Najeriya ta cancanci a girmama ta – Babban Hafsan Tsaro

Kylian Mbappe ne ya zama tauraro a wannan wasan, inda ya jefa wa Manchester City ƙwallaye uku rigis a raga.

Ɗan wasan gaban na Real Madrid, ya fara jefa ƙwallo ta farko a minti na 4 da fara wasa, sannan ya jefa ƙwallo ta biyu a minti na 33.

Bayan dawowa daga hutun rabin lokaci ne, Mbappe ya sake jefa ƙwallo ta uku a ragar Manchester City a minti 61.

A minti na 92 ɗan wasan Manchester City, Nico Gonzalez, ya warware mata ƙwallo ɗaya.

A haka wasan ya ƙare, amma Jude Bellingham ya samu katin gargaɗi, wanda hakan ke nufin ba zai buga wa Madrid wasanta na gaba a gasar ba.

Idan aka raba jadawalin ƙungiyoyin da za su kara da juna, Real Madrid za ta iya haɗuwa da Bayer Leverkusen ko Atletico Madrid.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gasar Zakarun Turai

এছাড়াও পড়ুন:

Gaza: Sojojin HKI Sun Sake Kai Wa Asibitin “Ma’amadani Hari

Jiragen yakin HKI sun harba makamai masu linzami guda biyu akan ginin asibitin Ma’amadani dake Gaza. Harin ya yi sanadiyyar rushewar wasu bangarori da su ka hada dakunan yin gwaje-gwaje da kantin sayar da magani.

 Saboda hare-haren na Isra’ila a wannan asibitin, da akwai gwamman marasa  lafiya da suke kwance a kasa a waje, yayin da wasu kuma suke kwance  wajen asibiti.

Kungiyar Hamas ta bayyana harin da sojojin HKI su ka kai wa asibitin da cewa wani sabon laifi ne na dabbanci da ‘yan sahayoniyar suka tafka a Gaza.

Haka nan kuma Kungiyar ta Hamas ta zargi Amurka da cewa ita ce take bai wa HKI haske akan tafka laifukan da take yi a Falasdinu.

 Bugu da kari kungiyar ta Hamas ta kuma yi mamaki akan yadda kungiyoyin kasa da kasa da su ka hada da MDD suke yin shiru akan laifukan da ake tafkawa da ba su da tamka a wannan zamanin, akan asibitoci da cibiyoyin kiwon lafiya da cutar da marasa lafiya da korarsu daga asibiti zuwa kan tituna.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu ya kaddamar da aikin sake gyaran titin Abuja zuwa Kano
  • Salah Ya Kafa Tarihi Yayin Da Liverpool Ke Dab Da Lashe Gasar Firimiya
  • An sake kama wasu mafarauta ’yan Kano a Jihar Edo
  • Badaƙalar Miyagun Ƙwayoyi: Kotun Amurka ta ba da umarnin fitar da bayanai kan binciken Tinubu
  • HKI Ta Jefa Boma-Bomai A Kan Asbiti Tilo Da Ya Rage Yake Aiki A Arewacin Gaza
  • Amnesty Ta Zargi  Rundunar “RSF” Ta Sudan Da Cin Zarafin Mata
  • Gaza: Sojojin HKI Sun Sake Kai Wa Asibitin “Ma’amadani Hari
  • Newcastle Na Gab Da Samun Gurbi A Gasar Zakarun Turai
  • Alex Iwobi Ya Kafa Tarihi A Gasar Firimiya
  • Isra’ila ta yi barazanar fadada hare-hare Gaza yayin da ta yanke Rafah daga birnin Khan Yunis