Real Madrid ta fitar da Man City a Gasar Zakarun Turai
Published: 20th, February 2025 GMT
Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Real Madrid ta sake doke Manchester City da ci 3 da 1 a filin wasa na Bernabeu.
Madrid ta karɓi baƙuncin Man City a wasan zagaye na biyu na gasar Zakarun Turai, bayan doke ta a gida da ci 3 da 2.
Gobara ta ƙone gidaje, dabobbi da kayan abinci a Kano Hana Biza: Najeriya ta cancanci a girmama ta – Babban Hafsan TsaroKylian Mbappe ne ya zama tauraro a wannan wasan, inda ya jefa wa Manchester City ƙwallaye uku rigis a raga.
Ɗan wasan gaban na Real Madrid, ya fara jefa ƙwallo ta farko a minti na 4 da fara wasa, sannan ya jefa ƙwallo ta biyu a minti na 33.
Bayan dawowa daga hutun rabin lokaci ne, Mbappe ya sake jefa ƙwallo ta uku a ragar Manchester City a minti 61.
A minti na 92 ɗan wasan Manchester City, Nico Gonzalez, ya warware mata ƙwallo ɗaya.
A haka wasan ya ƙare, amma Jude Bellingham ya samu katin gargaɗi, wanda hakan ke nufin ba zai buga wa Madrid wasanta na gaba a gasar ba.
Idan aka raba jadawalin ƙungiyoyin da za su kara da juna, Real Madrid za ta iya haɗuwa da Bayer Leverkusen ko Atletico Madrid.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gasar Zakarun Turai
এছাড়াও পড়ুন:
MDD Ta CE Sake Tada Komatsar Tattalin Arzikin Kasar Siriya Zau Dauki Shekaru 50 Nan Gaba
MDD ta bada sanarwan cewa tattalin arzikin kasar Siriya na bukatar shekaru 50 nan gaba kafin ta koma kamar yadda take kafin yakin basasa a kasar.
Tashar talabijan ta Presstv ta nakalato shugaban hukumar UNDP Achim Steiner yana fadar haka a jiya Alhamis, ta kuma kara da cewa hukumar ta ta gudanar da bincike kuma ta gano cewa, rikici da yakin basasa da kuma mamayar kasar da sojojin kasashen yamma suka yiwa kasar, ya sa al-amura sun lalace a kasar, ta yadda idan tana bukatar komawa matsayinta kafin shekara ta 2011 tana bukatar rabin karni kafin hakan ya samu. Wato kasar Siriya ba zata koma kamar yadda take a shekara ta 2011 ba sai nan da shekara 2080.
Tace Siriya tana bukatar zuba jari mai yawa a ko wace shekara kafin ta sami wannan ci gaban. A halin yanzu dai kasha 90% na mutanen kasar Siriya suna rayuwan talaka. Sannan kasha 50% daga cikinsu basa da aikin yi. Sannan tattalin arzikin kasar GDP na kasar yana rabin matsayinsa a shekara ta 2011. Banda tallafi daga kasashen waje kasar Siriya tana bukatar zuba jari mai yawa don komawa kamar yadda take.