Dubban Falasdinawa Sun Kauracewa Gidajensu A Dai-Dai Lokacinta Sojojin HKI Suke Fafatawa Da Dakarun Falasdinawa
Published: 20th, February 2025 GMT
Dubban Falasdinawa ne suka kauracewa gidajensu a yankin yamma da kogin Jordan. Tun ranar 21 ga watan Jeneru na wannan shekara ta 2025, wato kwanaki biyu kacal da tsaida wuta a Gaza, sojojin HKI suka fadawa sansanin yan gudun hijira na Jenen inda suka fara fafatawa da dakarun Falasdinawa a yankin. Da nufin korarsu.
Dagan nan ne dubban Falasdinawa suka fara kauracewa gidajensu a yankin. Wasu suka dauki dukkan iyalansu su a mota su tafi inda ba’a tashin hankali. Wasu kuma sukan taka da kafafuwansu zuwa nesa daga inda ake fada da tashin hankali.
Wani dan agaji a yankin ya bayyana wa Jaridar ‘Arabsnews’ cewa bai taba ganin irin wannan kaurar da Falasdinawa suke yi ba, sai wanda aka yi a yakin 1967 inda falasdinawa 300,000 suka kauracewa gidajensu, sai kuma kafin haka a shekara ta 1948 falasdinawa 700,000 ne, sojojin yahudawan suka tilastawa falasdinawa kauracewa yankunansu a kasarsu da aka mamaye.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Ranar Mata Ta Duniya: NPA Ta Mayar Da Hankali Wajen Kare ‘Yancin Mata –Dantsoho
Ya sanar da cewa, yanzu a Hukumar ana kara samun nada mata kan madafun iko, inda ya sanar da cewa, a yanzu a Hukumar mace ce, ke rike da mukamin Babbar Darakta ta sashen kudi da mulki wato uwargida Bibian C. Richard-Edet.
A cewarsa, a shekarun baya, akalla muna da mata sha biyu da suke rike da mukamain Janar Manaja da kuma mukamain Manajoji a Hukumar
Shugaban ya bayyana cewa, mata na ci gaba da bayar da gudunmawar su wajen habaka fannonin da ke a Hukumar ciki har da bangaren tsaro, kiwon lafiya da sauransu.
“Wadannan wasu misalai ne ‘yan kadan da Hukumar ke yi na inganta ‘yancin mata da tabbatar da ‘yancin su, duba da cewa, bamu iyakance irin kokarin da mata suke da shi ba,” A cewar Dantsoho.
Duk da samar da wadannan ci gaban a Hukumar Dantsoho ya bayyana cewa, Hukumar za ta ci gaba da sauye-sauyen da za su gaba da kare ‘yancin matan da ke aiki a Hukumar.
Kazalika, Dantsoho Hukumar ta NPA za ta ci gaba goyon bayan kare ‘yancin matan da ke aiki a Hukumar da kuma tallafa masu.
“A matsayin mu na Hukumar mun yi alkawarin ba za mu yi kasa a guiwa wajen goyon bayan ‘yancin mata da kuma ‘ya’ya mata da ke aiki a Hukumar, da kuma sauran matan da ba a Hukumar suke yin aiki ba,” Inji Dantsoho.
Dantso ya kuma taya matan da ke aiki a Hukumar murnar zagoyowar ranar ta mata ta duniya, inda ya ba su tabbacin cewa, Hukumar za ta ci gaba da zama a kan gaba wajen samar da damarmaki ga da ‘yan mata da ke a fannin.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp