HausaTv:
2025-03-23@23:36:02 GMT

Hamas Ta Ce Tana Iya Sakin Dukkan Fursinonin Yahudawa Gaba Daya A Lokaci Guda

Published: 20th, February 2025 GMT

Kungiya mai gwagwarmaya ta Falasdinawa Hamasa ta bayyana cewa tana iya sakin fursinoni yahudawa wadanda suke hannunta gaba daya a lokaci guda a marhala ta biyu ta musayar fursinoni tsakaninta da tare da sharadin ta cika al-kawulan da ta nauyi  alhakin aiwatar da shi a wannan karon. Daga cikin har da maida tsagaita wutan na din din din

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Taher Al-Nounou ya cewa idan an yi haka za’a kammala musayar fursononin gaba daya, sannan HKI ta sake duk fursinonin falasdinawa gaba daya da suke hannunta.

Yin hakan ya na nuna yanda al-amarin musayar Fursinoni yake da muhimmancin ga falasdinawa.

Kafin wannan sanarwan dai ministan yaki na HKI Isarael Katz ya bayyana cewa HKI tana shirin shiga tattaunawa ba gaba ba kai tsaye ba,  da Falasdinawa a marhala ta biyu da kungiyar Hamas, Ya kuma kara da cewa gwamnatinsa tana samun goyon bayan gwamnatin Amurka.

A zagaye na farko an musayar dai yahudawa 33 Hamas ta saka sannan  Falasdinawa kimani 2000  suka sami yanci.  Dakarun Qassam kadai ta saki yahudawa 19 a yayinda sauran kuma sauran kungiyoyin kuma sake sauran. A taunawa ta gaba ce za ta fayyace yadda tattaunawa ta gaba zata kasance.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kao Kim Hourn: Ba Ta Hanyar ‘Siddabaru’ Kasar Sin Ta Cimma Nasarori A Fannin Ci Gaba Ba Sai Dai Ta Hanyar Aiki Tukuru Kuma Mai Dorewa

A kwanan nan ne sakatare janar na kungiyar ASEAN Kao Kim Hourn ya bayyana a wata hirar da ya yi da wakilin babban gidan rediyo da talibijin na kasar Sin na CMG cewa, nasarorin da Sin ta samu ta fuskar ci gaba ba sakamakon ‘siddabaru’ ba ne, illa sakamakon aiki tukuru kuma mai dorewa.

Kao Kim Hourn, wanda ya ziyarci kasar Sin sau da dama, ya yi tsokaci kan abubuwan da ya gani a wadannan ziyarce-ziyarcensa. Ya bayyana cewa, tafiya daga filin jirgin sama zuwa tsakiyar gari, ya shaida yadda kasar Sin take da tsabta, da koren muhalli, da tsaro, da duk sakamakon ci gabanta na zahiri. Abin ban mamaki ne ganin yadda kasar Sin ta canza a cikin ‘yan shekarun nan. Abubuwan da ya gani a kasar Sin a cikin ‘yan shekarun nan sun matukar bambanta da abubuwan da ya gani lokacin da ya ziyarci kasar Sin a shekarun 1990.

Ya jaddada cewa, irin wadannan sauye-sauyen na nuna gagarumin kokari na bayan fage. Kana samun ci gaba yana bukatar aiki tukuru. Kao ya bayyana cewa, ci gaban da kasar Sin ta samu ne ba ta hanyar siddabaru ba, ta samu ne a sakamakon namijin kokarin da shugabannin kasar Sin da jama’arta suka yi. Ya kuma kara da cewa, ci gaban kasa yana bukatar kuzari mai yawa, da nagartaccen jagoranci, da dimbin albarkatu, da jajircewar al’ummarta. Kasar Sin misali ce ga hakan. (Mohammed Yahaya)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hanyoyi Goma Sha Daya Da Mace Za Ta Bi Domin Janyo Hankalin Mijinta
  • Ɗan sa-kai ya kashe matasa biyu a Borno
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [15]
  • EFCC Ta Cafke Mutum 21 Bisa Zarginsu Da Zambar Intanet A Bauchi
  • Kao Kim Hourn: Ba Ta Hanyar ‘Siddabaru’ Kasar Sin Ta Cimma Nasarori A Fannin Ci Gaba Ba Sai Dai Ta Hanyar Aiki Tukuru Kuma Mai Dorewa
  •  Haaretz: Sojojin Isra’ila Suna Kan Shirya Kai Wa Gaza Hari Ta Kasa
  • Kwana Daya Bayan Kwace Fadar Shugaban Kasa, Sojojin Sudan Sun Kwace Babban Bankin Kasar
  • An yi wa wata karya tiyatar ceton rai
  • Putin Ya Aike Wa Ayatullah Khamenei Da Murnar Idin Nowruz
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [13]