Hamas Za Ta Saki Dukkan Fursunonin Isra’ila Da Ke Hannunta
Published: 20th, February 2025 GMT
Hamas ta nuna shirin ta na sakin duk sauran fursunonin da take riƙe da su Gaza a cikin musanye guda cikin mataki na biyu na yarjejeniyar tsagaita wuta tsakaninnta da Isra’ila.
Babban Jami’in Hamas, Taher al-Nunu, ne ya bayyanawa masu shiga tsakani cewa ƙungiyar tana da niyyar sakin fursunonin gaba ɗaya maimakon rarraba su kashi-kashi kamar yadda aka yi a mataki na farko, wanda ya ce tabbaci ne da kuma shirinsu na ci gaba da warware batun.
A ƙarƙashin yarjejeniyar tsagaita wutar na yanzu, an saki fursunonin Isra’ila 19 a madadin fiye da Falasdinawa 1,100 da ke gidajen yari, wanda a yanzu fursunoni 58 ne za su rage a Gaza, sannan ana shirin mayar da gawarwakin fursunoni takwas da suka mutu cikin matakai biyu.
Ana sa ran mataki na biyu na yarjejeniyar zai fayyace matakan da za a ɗauka domin cimma cikakken tsagaita wuta, inda ake shirin fara tattaunawa a wannan mako.
এছাড়াও পড়ুন:
Noman rake: Najeriya da China sun kulla yarjejeniyar kasuwancin $1bn
Hukumar Bunƙasa Noman Sukari a Najeriya (NSDC) ta sanya hannu kan yarjejeniyar Dala biliyan guda da kamfanin SINOMACH na ƙasar China kan bunƙasa noman rake da sarrafa shi da nufin samar da sukari da kudina ya kai metrik ton miliyan guda.
Kulla yarjejeniyar wani ɓangare ne na shirin Kawancen Najeriya da China, na Gwmanatin Shugaba Bola Tinubu, da nufin kawo masu zuba jari na kimanin Dala biliyan guda a ɓangaren sukari a Najeriya.
Daga cikin yarjejeniyar, Kamfanin SINOMACH zai kafa masana’antar sukari da kuma gonar rake da za su fara da samar da metrik ton 100,000 na sukari a duk shekara.
Kamfanin zai kuma taimaka da kwarewarsa da kayayyakin aikinsa wajen zartar da abubuwan da suka danganci gine-gine sayayyan kayan aiki da ayyukan injiniyarin. Uwa uba, zai samar da kudaden ayyukan.
Matashi ya yi yunƙurin soka wa mahaifinsa makami a Kano Sojoji sun ceto mafiya 16 da aka yi garkuwa da wasu a FilatoA gefe guda kuma Hukumar NSDC za ta taimaka wajen samar da duk takardu da kuma sahalewar gwamnati da ake bukata domin fara aiki.
Da yake jawabi a taron sanya hannun a Abuja, Shugaban Hukumar, Kamal Bakrim ya bayyana cewa shekarar 2025 za ta kasance kashin baya ga samun bunkasar Najeriya.
“Shekara ce da muke sa ran samun gagarumar ci-gaba musamman a fannin tattalin arzikin da samar da wadataccena abinci a kasarmu.