Aminiya:
2025-04-14@17:44:38 GMT

An haramta wa manyan tireloli aiki a Najeriya

Published: 20th, February 2025 GMT

Gwmanatin Tarayya ta haramta wa tireloli masu ɗaukar man fetur da nauyinsa ya kai lita 60,000 aiki a Najeriya daga ranar 1 ga watan Maris mai kamawa.

Hukumar Albarkatun Man Fetur ta Kasa (NMDPRA) ta bayyana cewa an ɗauki matakin ne da nufin taƙaita yawan haɗuran tirelolin man fetur da ke sanadiyyar asarar ɗaruruwan rayuka da dukiyoyi na miliyoyin kuɗaɗe.

Hukumar ta ƙara da cewa zuwa ƙarshen wannan shekara ta 2025 za a haramta wa motoci masu ɗaukar man fetur lita 45,000 hawa titunan Najeriya.

Ta bayyana cewa bayan wani taron da aka gudanar kan yawan haɗuran tirelolin man fetur da irin asarar da hakan ke haifarwa, masu ruwa da tsaki a harkokin mai da sufuri hukumomin tsaro da sauransu sun yi ittifakin cewa a haramta wa tireloli masu ɗaukar man fetur da ya kai lita 60,000 hawa titi da kuma daukar mai a tashoshin sayar da man a faɗin Najeriya.

 

Ogbugo Ukoha, wanda shi ne Babban Daraktan Jigila na NMDPRA ya kara da cewar taron ya alaƙanta hatsarin motocin da nauyin kayan da motocin suke dauka kuma suka amince da ɗaukar matakin.

Ya bayyana cewa ƙaruwar hatsarin motocin musamman yadda ake samun asarar rayuka a lokacin da mutane ke zuwa kwasar man da ke tsiyaya.

Ukoha ya ce ganin yadda munin hatsarin ke ƙaruwa ya sa ɗaukar matakin ya zama dole.

Kungiyar NATO ta masu ababen haw ta koka da cewa matakin da gwamnati ta ɗauka zai jawo wa mambobinta asarar kimanin Naira biliyan 300.

Shugaban Ƙungiyar NATO, Yusuf Uthman, alaƙanta aukuwar haɗuran da rashin kyan hanyoyi da yanayin lafiyar motocin da kuma direbobi.

Ya ce mambobin kungiyar suna da tirela mai daukar lita 60,000 akalla guda 2,000 wadda kowacce kuɗinta ta kai Naira miliyan 150.

Don haka muddin aka hana motocin yin aiki to asarar da za su yi ta kai ta Naira biliyan 300.

Daga nan sai ya roki gwamnati ta shiga cikin lamarin ta hanyar saye motocin daga hannunsu domin rage musu raɗaɗi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Hatsari

এছাড়াও পড়ুন:

Najeriya Ta Jaddada Aniyar Aiwatar Da Sakamakon Taron FOCAC Na Beijing

 

Kazalika, mahalarta taron sun jaddada muhimmancin inganta samar da ayyukan yi, da karfafa tattalin arziki, da kyautata zaman rayuwar ’yan Najeriya, ta hanyar kulla huldar abokantaka bisa manyan tsare-tsare da kasar Sin. (Mohammed Yahaya)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin Yemen Sun Kakkabo Jirgin Yakin Amurka Wanda Ake Sarrafa Shi Daga Nesa Na 19
  • Brice Ologui Ya Lashe Zaben Shugaban Kasar Gaban Da Kashi 90.35% A Jiya Lahadi
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Farfaɗowar Boko Haram A Jihar Borno
  • Xi Da Prabowo Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 75 Da Kulla Huldar Diplomasiyya Tsakanin Sin Da Indonesiya
  • A daina cutar ’yan Najeriya ta hanyar rabon kayan tallafi
  • HKI Ta Jefa Boma-Bomai A Kan Asbiti Tilo Da Ya Rage Yake Aiki A Arewacin Gaza
  • ‘Tell Your Papa’: NBC ta haramta amfani da waƙar da ke sukar Tinubu
  •  Limamin Tehran: Iran Ba Ta Tsoron Tattaunawa
  • Najeriya Ta Jaddada Aniyar Aiwatar Da Sakamakon Taron FOCAC Na Beijing
  • Atiku ya jagoranci manyan ’yan siyasa sun ziyarci Buhari