An haramta wa manyan tireloli aiki a Najeriya
Published: 20th, February 2025 GMT
Gwmanatin Tarayya ta haramta wa tireloli masu ɗaukar man fetur da nauyinsa ya kai lita 60,000 aiki a Najeriya daga ranar 1 ga watan Maris mai kamawa.
Hukumar Albarkatun Man Fetur ta Kasa (NMDPRA) ta bayyana cewa an ɗauki matakin ne da nufin taƙaita yawan haɗuran tirelolin man fetur da ke sanadiyyar asarar ɗaruruwan rayuka da dukiyoyi na miliyoyin kuɗaɗe.
Hukumar ta ƙara da cewa zuwa ƙarshen wannan shekara ta 2025 za a haramta wa motoci masu ɗaukar man fetur lita 45,000 hawa titunan Najeriya.
Ta bayyana cewa bayan wani taron da aka gudanar kan yawan haɗuran tirelolin man fetur da irin asarar da hakan ke haifarwa, masu ruwa da tsaki a harkokin mai da sufuri hukumomin tsaro da sauransu sun yi ittifakin cewa a haramta wa tireloli masu ɗaukar man fetur da ya kai lita 60,000 hawa titi da kuma daukar mai a tashoshin sayar da man a faɗin Najeriya.
Ogbugo Ukoha, wanda shi ne Babban Daraktan Jigila na NMDPRA ya kara da cewar taron ya alaƙanta hatsarin motocin da nauyin kayan da motocin suke dauka kuma suka amince da ɗaukar matakin.
Ya bayyana cewa ƙaruwar hatsarin motocin musamman yadda ake samun asarar rayuka a lokacin da mutane ke zuwa kwasar man da ke tsiyaya.
Ukoha ya ce ganin yadda munin hatsarin ke ƙaruwa ya sa ɗaukar matakin ya zama dole.
Kungiyar NATO ta masu ababen haw ta koka da cewa matakin da gwamnati ta ɗauka zai jawo wa mambobinta asarar kimanin Naira biliyan 300.
Shugaban Ƙungiyar NATO, Yusuf Uthman, alaƙanta aukuwar haɗuran da rashin kyan hanyoyi da yanayin lafiyar motocin da kuma direbobi.
Ya ce mambobin kungiyar suna da tirela mai daukar lita 60,000 akalla guda 2,000 wadda kowacce kuɗinta ta kai Naira miliyan 150.
Don haka muddin aka hana motocin yin aiki to asarar da za su yi ta kai ta Naira biliyan 300.
Daga nan sai ya roki gwamnati ta shiga cikin lamarin ta hanyar saye motocin daga hannunsu domin rage musu raɗaɗi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Hatsari
এছাড়াও পড়ুন:
Fiye Da Dalibai 4,200 Suka Amfana Da Tallafin Ilimi Na Sanata Solomon Adeola
Ya kara bayanin cewa an dauki matakin ne inda har abin ya shafi daliban da suke mazabun majalisar Dattawa biyu na Jihar Osun.
Ya nuna jin dadinsa inda ya furta ce wa“Wani abin farinciki ne gare ni dana samu yawan daliban da suka samu damar yin rajista daga mazaba ta da kuma saiuran mazabun na majalisar Dattawa, wadanda su basu samu damar rubuta jarabawar da zata basu damar zuwa manyan makarantu ba a fadin tarayyar Nijeriya.
“Ilimi shi ne wani babban abinda ya kamata kowane dan/ ‘yar kasa su kasance sun samu damar yin haka ta samun sa, don haka lamarain kudi bai dace ace ya hana su damar samun hakan ba musamman ma ga matasa wadanda sune manyan gobe kamar yadda Sanatan ya bayyana”.
Daga karshe ya yi karin bayani ne na shit sarin bada fom domin cikawa saboda rubuta JAMB wata dama ce ita ma tayi kama ko daya take da damar bada guraben karatu zuwa manyan makarantu, na dalibai 500 za a cimma burin yin haka cikin makonni masu zuwa na gaba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp