Aminiya:
2025-03-24@11:30:59 GMT

’Yan bindiga sun kashe mutum 12, sun sace wasu a Zariya

Published: 20th, February 2025 GMT

’Yan bindiga sun kashe wasu ’yan kasuwar Gwari 12, tare da sace wasu yayin da suke kan hanyarsu ta komawa Zariya bayan cin kasuwa.

Lamarin ya faru ne a ƙauyen Tafoki da ke Jihar Katsina, bayan ’yan bindigar sun buɗe wa motarsu wuta.

An haramta wa manyan tireloli aiki a Najeriya Jami’an tsaron al’umma 6 sun mutu a artabu da ’yan bindiga a Sakkwato

Masu sana’ar Gwari da abin ya shafa ’yan kasuwar Ɗan Magaji ne daga Ƙaramar Hukumar Zariya, a Jihar Kaduna.

Aminiya ta tattauna da wasu daga cikin waɗanda suka tsira, waɗanda suka ji raunuka, da kuma waɗanda aka sako bayan biyan kuɗin fansa Naira miliyan biyu.

Muhammad Zaharraddeen Sharaihu shi ne mutumin da ya kai wa ’yan bindigar kuɗin fansa domin a sako mahaifinsa da wasu mutum uku da aka yi garkuwa da su a dajin Katsina.

Zaharraddeen, ya ce tun yana kan hanya ‘yan bindigar suka riƙa kiran wayarsa har sai da ya isa inda suka ce ya tsaya.

Daga nan suka umarce shi da ya hau babur, sannan suka ce ya tsaya a wani waje don miƙa musu kuɗin.

Bayan ya miƙa kuɗin, wani mutum ya karɓa daga hannunsa, sannan aka umarce shi da ya koma bakin hanya ya jira fitowar ’yan uwansa.

A cewarsa, tun ƙarfe 1 na rana sai kusan Magariba aka sako mahaifinsa da sauran mutanen da aka yi garkuwa da su.

Mutum huɗu da aka biya miliyan biyu kafin a sako su sun haɗa da Malam Sharihu Umar Shehi, Malam Magaji Idris, Lawal Gambo Kwalano da Ida Ɗan Gwari

Lamarin ya ƙara dagula yanayin tsaro a yankin, inda jama’a ke fargabar ci gaba da ayyukan kasuwancinsu a yankunan da ke fama da hare-haren ’yan bindiga.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga yan kasuwa Garkuwa Gwari Zariya yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Za’a Gudanar Taron Tattaunawa Tsakanin Rasha Ta Amurka A Karo Na Biyu 2 A Birnin Rayad na Kasar Saudiya

A gobe Litinin 24 ga watan Maris ne tawagogin masu tattaunawa na kasashen Amurka da Rasha zasu hadu a birnin Rayida na kasar Saudiya don ci gaba da tattaunawan da suka fara a yan makonnin da suka gabata dangane da yakin da ke faruwa a Ukraine, shekaru fiye da 3 da suka gabata, da kuma dangantaka a tsakanin kasashen biyu.

Kamfanin dillancin labaran Sputnik na kasar Rasha ya nakalto Yury Ushakov mai bawa shugaba Putin shawara kan al-amurin siyasa yana fadar haka. Ya kuma kara da cewa Sanata Georgy Karasin ne zai jagoranci tawagar masu tattaunawa ta kasar Rasha sannan ta kasar Amurka an rika an samar da tawagar, wasu zata hadu da na Rasga a gobe litin a birnin Riyad.

Kafin haka dai shugaban kasar Rasha Vladimir Putin sun tattauna da tokwaransa na kasar Amurka Donal Trump kan al-amura da dama wadanda suka shafi yakin a Ukraine da tsagaita budewa juna wuta na wata guda da kuma wasu al-amura.

Karsin daga karshe ya ce yana fatan tattaunawan zata yi armashi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ɗansanda Ya Kashe Matar Abokin Aikinsa, Ya Jikata Wasu Biyu A Ribas
  • Wasu manyan ’yan Nijeriya sun yi wa Gwamna Radda ta’aziyya a Saudiyya
  • Za’a Gudanar Taron Tattaunawa Tsakanin Rasha Ta Amurka A Karo Na Biyu 2 A Birnin Rayad na Kasar Saudiya
  • ’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 10, sun jikkata 14 a Zamfara
  • An ayyana zaman makoki na kwana uku bayan kashe mutum 44 a Nijar
  • Gwamnati ta kama mutum 347 kan haƙar ma’adanai ba bisa ƙa’ida ba
  • ’Yan bindiga sun hallaka matashi ana sallar Tahajjud a Kaduna
  • Bam ya kashe mutum 4 da jikkata wasu a Borno
  • ’Yan bindiga sun yi garkuwa da jami’in FRSC a Benuwe
  • Sojoji sun ceto mutum 84 da ’yan bindiga suka sace a Katsina