Aminiya:
2025-02-22@06:35:38 GMT

Majalisa ta fara bincike kan zargin USAID na tallafa wa Boko Haram

Published: 20th, February 2025 GMT

Majalisar Wakilai ta kafa kwamiti na musamman da zai binciki zargin da ake yi wa Hukumar Bayar da Agaji ta Ƙasa da Ƙasa ta Amurka (USAID), da tallafa wa Boko Haram.

An yanke wannan hukunci ne bayan ɗan majalisa, Inuwa Garba, ya gabatar da buƙatar gaggawa a zaman majalisar na ranar Alhamis.

’Yan bindiga sun kashe mutum 12, sun sace wasu a Zariya Hisbah ta rufe gidajen rawa a Katsina

Garba, ya nuna damuwa game da kalaman da ɗan majalisar dokokin Amurka, Scott Perry, ya yi kwanan nan, inda ya zargi USAID da bai wa ƙungiyoyin ’yan ta’adda, ciki har da Boko Haram tallafi.

Ya jaddada cewa Boko Haram ta haddasa babbar matsalar tsaro a Najeriya sama da shekara 10.

“Scott Perry ya yi wannan iƙirari a wani zaman majalisar dokokin Amurka, inda ya ce ana kashe sama da dala miliyan 697 duk shekara, kuma kai-tsaye ga ƙungiyoyi irin su ISIS, Al-Qaeda, da Boko Haram ne suke amfana,” in ji Garba.

“Boko Haram na da babbar maɓoya a Arewacin Najeriya, don haka akwai yiyuwar sun amfana da wannan tallafi.

“Idan zargin ya kasance gaskiya, hakan babbar barazana ce ga tsaron ƙasa da na duniya baki ɗaya,” in ji shi.

Bayan tattaunawa tsakanin ’yan majalisar, Kakakin Majalisar ya kafa kwamitin bincike na musamman don yin duba a kan lamarin.

Ana sa ran kwamitin zai gabatar da rahotonsa cikin makonni biyu masu zuwa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Boko Haram Ɗaukar Nawa Kwamiti Majalisar Wakilai

এছাড়াও পড়ুন:

An tara Naira 16 a taron ƙaddamar da littafin IBB

Hamshakan attajirai da ’yan siyasa sun bayar da gudunmawar sama da Naira biliyan 16 a bikin kaddamar da littafin tarihin tsohon shugaban ƙasa na mulkin soja, Janar Ibrahim Badamasi Babangida.

Taron ƙaddamar da littafin, mai suna ‘A Journey in Service’, wanda aka gudanar a Abuja ya tara manyan baƙi daga ciki da wajen Najeriya.

Mahalarta taron da aka gudanar a Abuja ranar Alhamis sun bayar da gudunmawar ne domin ginin dakin karatun da tsohon shugaban ƙasan ke shirin ginawa. Attajiri mafi yawan arziki a Afirka kuma Shugaban Rukunin Kamfanonin Ɗangote, Alhaji Alikon Ɗangote ya ba da gudunmawar Naira biliyan takwas, Naira biliyan biyu a duk shekara, na tsawon shekara huɗu. Ya kuma yi alƙawarin karin biliyan biyu a duk shekara har a gama aikin. NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Ba Za Mu Sauke Farashin Burodi Ba —’Yan kasuwa Ba ni da hannu a kisan Dele Giwa — Janar Babangida

A nasa ɓangaren, Shugaban Rukunin Kamfanonin BUA, ya ba da gudunmawar Naira biliyan biyar.

Tsohon Ministan Taro kuma Shugaban Gidauniyar TY, Janar Theophelus Ɗanjuma, ya bayar da Naira biliyan uku.

Babban attajiri a yankin Kudu, Arthur Eze, ya ba da Naira miliyan 500.

Sanata Sani Musa ya ba da miliyan N250 a yayin da Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya ba da miliyan N50.

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa Sanata Barau Jibrin ya ba da Naira miliyan 20 a yayin da Sanata Aliyu Wadada ya ba da miliyan 10.

Hamshakiyar ’yan kasuwa Folorunsho Alakija, da wasu fitattun ’yan Najeriya sun bayyana gudunmawa, amma ba su sanarna bainar jama’a ba.

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya jagoranci tsoffin shugaban kasa na farar hula na mulkin soji irinsu Goodluck Jonathan, Yakubu Gowon, Abdulsalami Abubakar, da wasu manyan baƙi.

Tsoffin mataimakan shugaban kasa Alhaji Atiku Abubakar da Muhammad Namadi Sambo da Yemi Osinbajo.

Hakazalika dan takarar shugaban ƙasa na Jam’iyyar NNPP Sanata Rabiu Musa Kwankwaso da takwaransa na Jam’iyyar LP, Peter Obi, sun samu halartar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An tara Naira 16 a taron ƙaddamar da littafin IBB
  • INEC Ta Buƙaci Majalisa Ta kirkiro Dokar Hana ‘Yan Siyasa Zuwa Rumfunan Zabe Da Maƙudan Kuɗaɗe
  • Ministoci Za Su Fara Gabatar Da Rahoton Ayyuka A Taron Manema Labarai  
  • NNPP ta rasa Ɗan Majalisa na farko da ya koma APC
  • Zargin Daukar Nauyin Boko Haram: Tinubu Na Ganawar Sirri Da Akpabio A Villa
  • Ukraine ce mai laifi a yaƙin da ta ke yi da Rasha — Trump
  • Mutum 11 sun kuɓuta daga hannun Boko Haram a Borno
  • Majalisar Edo ta tanadi hukuncin kisa kan masu garkuwa da mutane
  • USAID: Amurka za ta yi bincike kan ɗaukar nauyin Boko Haram