Aminiya:
2025-04-14@18:00:54 GMT

Majalisa ta fara bincike kan zargin USAID na tallafa wa Boko Haram

Published: 20th, February 2025 GMT

Majalisar Wakilai ta kafa kwamiti na musamman da zai binciki zargin da ake yi wa Hukumar Bayar da Agaji ta Ƙasa da Ƙasa ta Amurka (USAID), da tallafa wa Boko Haram.

An yanke wannan hukunci ne bayan ɗan majalisa, Inuwa Garba, ya gabatar da buƙatar gaggawa a zaman majalisar na ranar Alhamis.

’Yan bindiga sun kashe mutum 12, sun sace wasu a Zariya Hisbah ta rufe gidajen rawa a Katsina

Garba, ya nuna damuwa game da kalaman da ɗan majalisar dokokin Amurka, Scott Perry, ya yi kwanan nan, inda ya zargi USAID da bai wa ƙungiyoyin ’yan ta’adda, ciki har da Boko Haram tallafi.

Ya jaddada cewa Boko Haram ta haddasa babbar matsalar tsaro a Najeriya sama da shekara 10.

“Scott Perry ya yi wannan iƙirari a wani zaman majalisar dokokin Amurka, inda ya ce ana kashe sama da dala miliyan 697 duk shekara, kuma kai-tsaye ga ƙungiyoyi irin su ISIS, Al-Qaeda, da Boko Haram ne suke amfana,” in ji Garba.

“Boko Haram na da babbar maɓoya a Arewacin Najeriya, don haka akwai yiyuwar sun amfana da wannan tallafi.

“Idan zargin ya kasance gaskiya, hakan babbar barazana ce ga tsaron ƙasa da na duniya baki ɗaya,” in ji shi.

Bayan tattaunawa tsakanin ’yan majalisar, Kakakin Majalisar ya kafa kwamitin bincike na musamman don yin duba a kan lamarin.

Ana sa ran kwamitin zai gabatar da rahotonsa cikin makonni biyu masu zuwa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Boko Haram Ɗaukar Nawa Kwamiti Majalisar Wakilai

এছাড়াও পড়ুন:

Kallo Daya Mutum Za Yi Min Ya Gane Masana’antar Kannywood Ta Canza Rayuwata -Farida Abdullahi

Daga karshe ta ce da farko ta samu turjiya daga wajen wasu mutane a kan kudurinta na fara harkar fim amma kuma ta yi biris dasu ta fara, amma kuma yanzu wadanda a baya ke hanata shiga fim su ne yanzu ke yi mata murnar samun nasara hakan ya matukar bata mamaki, duba da cewar wadanda ta ke tunanin za su tsaneta kasancewarta jarumar fim sun zamo masoyanta.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yansanda Sun Kama Wani Kato Bisa Zargin Cin Zarafin Wata Mata A Adamawa
  • ‘Yansanda Sun Kama Wasu Da Ake Zargin Ɓarayin Wayar Wutar Lantarki Ne A Yobe
  • Boko Haram ta kashe mutum 300 ta kwace ƙananan hukumomi 3 a Borno — Ndume
  • Abincin karnuka ya fi namu —Fursunonin Najeriya
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Farfaɗowar Boko Haram A Jihar Borno
  • ’Yan adawa sun zama kyanwar Lami duk da rinjayensu a Majalisa
  • Kallo Daya Mutum Za Yi Min Ya Gane Masana’antar Kannywood Ta Canza Rayuwata -Farida Abdullahi
  • Mahaifi ya yi wa ’yarsa ciki a Bauchi
  • ‘Yan Boko Haram Na Ci Gaba Da Mamaye Sassan Jihar Borno -Zulum
  • An kashe mutum kan zargin satar kare a Bauchi