Aminiya:
2025-04-16@00:26:13 GMT

Na yi nadamar soke zaɓen 1993 — Babangida

Published: 20th, February 2025 GMT

Tsohon Shugaban Mulkin Soja na Najeriya, Ibrahim Badamasi Babangida, ya ce ya yi nadamar soke zaɓen shugaban ƙasa na ranar 12 ga watan Yunin 1993.

Ya ce da zai samu wata dama da zai yanke wani hukunci daban.

Harin ’Yan bindiga: Mun yi asarar shanu sama da miliyan 4 – Miyetti Allah Majalisa ta fara bincike kan zargin USAID na tallafa wa Boko Haram

Babangida ya bayyana hakan ne a Abuja a ranar Alhamis, yayin ƙaddamar da littafin tarihin rayuwarsa mai suna ‘A Journey in Service’.

Yayin da tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Yemi Osinbajo, ke nazarin littafin, Babangida ya amsa alhakin soke zaɓen da aka gudanar tsakanin Moshood Abiola na jam’iyyar Social Democratic Party (SDP) da Bashir Tofa na jam’iyyar National Republican Convention (NRC).

“Ina nadamar soke zaɓen ranar 12 ga watan Yuni. Na ɗauki alhakin matakin da aka ɗauka, domin hakan ya faru ne a ƙarƙashina ikona.

“Mun yi kuskure, kuma abubuwa sun faru cikin gaggawa,” in ji Babangida.

A baya, Babangida ya taɓa kare matakin soke zaɓen, inda ya ce an gudanar da shi cikin gaskiya da adalci, wanda a cewarsa Najeriya ba ta shirya karɓar mulkin dimokuraɗiyya ba a wancan lokaci.

“12 ga watan Yuni shi ne zaɓen mafi kyau a tarihin Najeriya—an yi shi cikin gaskiya da adalci. Amma abin takaici, dole muka soke shi.

“A lokacin, mun fahimci hatsarin miƙa mulki ga gwamnatin dimokuraɗiyya. Mun yi tsoron cewa idan muka miƙa mulki, cikin watanni shida, wani juyin mulki zai sake faruwa, kuma hakan zai zama gazawa a ɓangarenmu,” in ji shi.

Babangida, ya ƙara da cewa bayan soke zaɓen, gwamnatinsa ta shirya gudanar da wani sabon zaɓe a watan Nuwamban 1993.

Amma saboda tarzomar da ta biyo bayan soke zaɓen, ba a samu damar yin wani zaɓen ba.

A cewarsa a maimakon haka, sun kafa gwamnatin riƙon ƙwarya, amma daga baya, Janar Sani Abacha ya hamɓarar da ita.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Soke Zaɓe Zaɓen 1993 soke zaɓen

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun kona masallacin Juma’a da asibiti da gidaje da Zamfara

’Yan bindiga sun kona masallacin Juma’a da asibiti da gidaje fiya da 10 a yankin Biyabiki da ke Karamar Hukumar Tsafe ta Jihar Zamfara.

’Yan ta’addan sun cinna kona wuraren ne bayan sallar Isha’i a ranar Asabar a wani da ake zargin na ramuwar gayya ne kan kashe Isuhu Yellow, kanin wani jagoran ’yan bindiga mai suna Adamu Aliero.

Shaida sun ce da  misalin karfe 8 na dare ne ’yan bindigar da ake zargin yaran kasurgumin dan bindiga Adamu Aliero ne suka kai harin a kan babura, inda suka banka wa wuraren wuraren wuta, sannan suka tsere ba tare da taba mazauna ba.

“Wuraren da suka cinna wa wuta sun hada da masallacin Juma’a da wani karamin asibiti da kuma gidaje kimanin 10 da suka lalata,” in ji wani mazaunin garin da ya nemi a boye sunansa.

A daina cutar ’yan Najeriya ta hanyar rabon kayan tallafi ’Yan adawa sun zama kyanwar Lami duk da rinjayensu a Majalisa

Ana kyatuta zaton harin na da alaka da kashe Adamu Yelow a wani harin kwanton bauna da shi da tawagarsa suka kai wa jami’an tsaro, a yankin Keta, kimanin makonni uku da suka gabata, amma jami’an tsaron suka aika su lahira.

Tun da farko a ranar sai da ’yan ta’addan sun kuma kai wani hari a kauyen Tsageru a ranar, inda suka kona gidaje da dama.

Wani mazaunin yankin ya ce, “Ba mu san wace butaka suke neman cim ma da kona gidaje da kayan gwamnati da suke yi ba; Tun da aka kashe Isuhu Yellow yankunanmu ke ta fuskantar barazana, don haka muna kyatata zaton wanna harin ramuwar gayya ce.”

Wakilinmu ya yi kokarin tattaunawa da kakakin ’yan sanda na Jihar Zamfara, DSP Yazid Abubakar, domin samun karin bayani, amma hakarsa ba ta cimma ruwa ba, bayan ya yi ta kiran wayar jami’in.

Wannan hari na kara nuna alamr ci gaban matsalar tsao a Jihar Zamfara inda ’yan bindiga ke kara cin karensu a yankunan karkara, duk kuwa da kokarin hukumomin tsaro na yi wa tufkar hanci a yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hajj 2025: Hukumar Alhazai Ta Shirya Taron Bita Ga Mahajjata a Jihar Kwara
  • Lauyoyin London Suna Tattara Bayanai Kan ‘Yan Birtaniya Da Suka Yi  Yaki Cikin Sahun Yahudawan Sahayoniyya A Gaza
  • Hauhawar Farashi ya ƙaru a watan Maris — NBS
  • Duk da samun koma baya: Najeriya ce kasa mafi arzikin danyen mai a Afirka —OPEC
  • Isra’ila ta kashe Palasdinawa 17 ta jikkata 69 a awa 24 a Gaza
  • Aljeriya ta yi barazanar korar jami’an diflomasiyyar Faransa 12
  • Iran Ta Ce Za’a Gudanar Da Zagaye Na Gaba Tsakaninta Da Amurka Ne A Birnin Roma Na Kasar Italiya
  • Al’ummar Mauritaniya Sun Gudanar Da Zanga-Zangar Nuna Adawa Da Yakin Gaza
  • ’Yan bindiga sun kona masallacin Juma’a da asibiti da gidaje da Zamfara
  • Badaƙalar Miyagun Ƙwayoyi: Kotun Amurka ta ba da umarnin fitar da bayanai kan binciken Tinubu