Aminiya:
2025-03-25@13:58:06 GMT

Na yi nadamar soke zaɓen 1993 — Babangida

Published: 20th, February 2025 GMT

Tsohon Shugaban Mulkin Soja na Najeriya, Ibrahim Badamasi Babangida, ya ce ya yi nadamar soke zaɓen shugaban ƙasa na ranar 12 ga watan Yunin 1993.

Ya ce da zai samu wata dama da zai yanke wani hukunci daban.

Harin ’Yan bindiga: Mun yi asarar shanu sama da miliyan 4 – Miyetti Allah Majalisa ta fara bincike kan zargin USAID na tallafa wa Boko Haram

Babangida ya bayyana hakan ne a Abuja a ranar Alhamis, yayin ƙaddamar da littafin tarihin rayuwarsa mai suna ‘A Journey in Service’.

Yayin da tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Yemi Osinbajo, ke nazarin littafin, Babangida ya amsa alhakin soke zaɓen da aka gudanar tsakanin Moshood Abiola na jam’iyyar Social Democratic Party (SDP) da Bashir Tofa na jam’iyyar National Republican Convention (NRC).

“Ina nadamar soke zaɓen ranar 12 ga watan Yuni. Na ɗauki alhakin matakin da aka ɗauka, domin hakan ya faru ne a ƙarƙashina ikona.

“Mun yi kuskure, kuma abubuwa sun faru cikin gaggawa,” in ji Babangida.

A baya, Babangida ya taɓa kare matakin soke zaɓen, inda ya ce an gudanar da shi cikin gaskiya da adalci, wanda a cewarsa Najeriya ba ta shirya karɓar mulkin dimokuraɗiyya ba a wancan lokaci.

“12 ga watan Yuni shi ne zaɓen mafi kyau a tarihin Najeriya—an yi shi cikin gaskiya da adalci. Amma abin takaici, dole muka soke shi.

“A lokacin, mun fahimci hatsarin miƙa mulki ga gwamnatin dimokuraɗiyya. Mun yi tsoron cewa idan muka miƙa mulki, cikin watanni shida, wani juyin mulki zai sake faruwa, kuma hakan zai zama gazawa a ɓangarenmu,” in ji shi.

Babangida, ya ƙara da cewa bayan soke zaɓen, gwamnatinsa ta shirya gudanar da wani sabon zaɓe a watan Nuwamban 1993.

Amma saboda tarzomar da ta biyo bayan soke zaɓen, ba a samu damar yin wani zaɓen ba.

A cewarsa a maimakon haka, sun kafa gwamnatin riƙon ƙwarya, amma daga baya, Janar Sani Abacha ya hamɓarar da ita.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Soke Zaɓe Zaɓen 1993 soke zaɓen

এছাড়াও পড়ুন:

Matasa sun kashe yaron da suka yi garkuwa da shi a Bauchi

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Bauchi, ta kama wasu matasa huɗu da ake zargi da yin garkuwa da kuma kashe wani yaro ɗan shekara shida, Shuaibu Safiyanu, a ƙauyen Sade da ke Ƙaramar Hukumar Darazo.

Aminiya ta ruwaito cewar mahaifin yaron, Safiyanu Abdullahi ne, ya sanar da Sarkin garinsu, Musa Isah, cewa a ranar 20 ga watan Maris, 2025, ɗansa ya ɓace.

Ɗan sa-kai ya kashe matasa biyu a Borno Gwamnatin Jigawa ta ƙaddamar da shirin noman rani na Lallashi

Washegari, wani ya kira shi a waya yana neman kuɗin fansa.

Da farko, ya nemi miliyan uku (₦3,000,000), amma daga baya suka rage zuwa Naira dubu ɗari biyu (₦200,000).

A ranar 21 ga watan Maris, aka gano gawar yaron a cikin daji, an ɗaure masa wuya da igiya.

Nan take aka kai shi asibiti, inda likitoci suka tabbatar da mutuwarsa.

Daga nan aka bai wa iyalansa gawarsa domin yi masa jana’iza.

Kakakin ’yan sandan Jihar, CSP Ahmed Mohammed Wakil, ya ce bayan samun rahoton lamarin, jami’an su suka fara bincike.

Sun fara binciken ne daga wajen POS da ke kusa da inda aka buƙaci a biya kuɗin fansar.

A yayin binciken, sun kama wani matashi mai shekara 23, Rabi’u Muhammadu daga ƙauyen Leka.

An gano cewa lambar wayarsa ce aka yi amfani da ita wajen kiran mahaifin yaron.

Sannan ’yan sanda sun gano asusun bankin da aka bayar don biyan kuɗin fansar: Lambar asusu: 0145285130 Sunan mai asusu: Ozochikelu Samson Banki: Union Bank PLC

Bayan kama Rabi’u, ya bayyana cewa Samson Ozochikel, mai shekara 35 daga ƙauyen Sade, shi ne ya shirya yadda za a sace yaron.

Ya kuma ambaci wasu matasa biyu, Muhammad Sani (Jingi), mai shekara 25, da Musa Usman (Kala), mai shekara 30, dukkaninsu daga ƙauyen Leka.

A halin yanzu, ’yan sanda suna tsare da su, kuma ana ci gaba da bincike a sashen binciken manyan laifuka (SCID).

Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar, ya tabbatar da cewa za su tabbatar da an yi adalci.

Ya kuma roƙi jama’a da su ci gaba da bai wa ’yan sanda haɗin kai, tare da sanar da su duk wani abun zargi ta layin kiran wayar gaggawa 112 ko Police Control Room a lamba 08156814656.

Rundunar ta jaddada ƙudirinta na kare rayuka da dukiyar al’ummar jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [17]
  • Ana ci gaba da gudanar da zanga-zangar goyon bayan Falastinu a kasashen duniya
  • NAJERIYA A YAU: Yadda watan Ramadana ke tasiri a harkokin kasuwanci
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [16]
  • Za’a Gudanar Taron Tattaunawa Tsakanin Rasha Ta Amurka A Karo Na Biyu 2 A Birnin Rayad na Kasar Saudiya
  • ’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 10, sun jikkata 14 a Zamfara
  • An shiga ruɗani yayin da Sanusi II da Bayero ke shirin hawan salla a Kano
  • Matasa sun kashe yaron da suka yi garkuwa da shi a Bauchi
  • Isra’ila ta kashe wani mamba na ofishin siyasa na Hamas
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [15]