Jakadan Sin dake kasar Najeriya Yu Dunhai ya gana da karamar ministar harkokin waje ta kasar Bianca Odumegu-Ojukwu.

Jakada Yu ya bayyana cewa, a shekarar bara, shugaban kasar Sin Xi Jinping da shugaban kasar Najeriya Bola Tinubu, sun sanar da inganta dangantakar dake tsakanin Sin da Najeriya zuwa dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare a dukkan fannoni, wanda ya zama babban ci gaba ga raya dangantakar dake tsakanin kasashen biyu.

A farkon shekarar bana kuma, memban hukumar kula da harkokin siyasa ta kwamitin tsakiya na jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin kuma ministan harkokin wajen kasar Wang Yi ya kai ziyara Najeriya cikin nasara, hakan ya kara kyautata dangantakar dake tsakanin kasashen biyu zuwa sabon matsayi. A cewar jakadan, Sin tana son hada shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya da manufar fatan samun farfadowa ta Najeriya, da kara hadin gwiwa bisa manufofin raya kasashen biyu, da raya manufar makomar bai daya ta Sin da Najeriya mai inganci, yana mai cewa, ta hakan za su taka muhimmiyar rawa wajen sa kaimi ga hadin gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa a duniya.

A nata bangare, madam Bianca Odumegu-Ojukwu ta bayyana cewa, shugaba Tinubu ya kai ziyara kasar Sin a shekarar bara, lamarin da ya shaida cewa, Najeriya tana maida hankali ga raya dangantakar dake tsakaninta da Sin. Ta ce kasar Najeriya ta tsaya tsayin daka kan manufar Sin daya tak, kuma tana son hada hannu da kasar Sin wajen aiwatar da ayyukan da aka cimma a ganawar shugabannin kasashen biyu da taron koli na dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka na Beijing, ta yadda za a inganta hadin gwiwar kasashen biyu har ya amfanawa jama’arsu baki daya. (Zainab Zhang)

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: dangantakar dake tsakanin

এছাড়াও পড়ুন:

An Bude Taron Shekara-Shekara Na Dandalin Tattauna Raya Kasa Na Sin Na 2025

A yau Lahadi ne aka bude taron shekara-shekara na dandalin tattauna raya kasa na kasar Sin na 2025 a nan birnin Beijing, taron da cibiyar binciken raya kasa ta majalisar gudanarwar kasar Sin ta shirya tare da hadin gwiwar asusun binciken raya kasa na kasar Sin. Firaministan kasar Sin Li Qiang ya halarci bikin bude taron, inda ya gabatar da muhimmin jawabi, wanda a cikinsa ya jaddada aniyar kasar Sin ta kara bude kofa ga kasashen waje.

Shi ma mataimakin darektan ofishin kula da harkokin yau da kullum na hukumar kudi da tattalin arziki ta kwamitin kolin JKS Han Wenxiu, wanda ya halarci taron na shekara-shekara, ya ce kasar Sin za ta dauki dukkan matakai na habaka kashe kudi, da kuma ci gaba da haifar da yanayi, ta yadda ingantaccen ci gaba da kyakkyawar rayuwa za su rika karfafar juna.

Hajiya Safara’u, Mahaifiyar Gwamna Raɗɗa Ta Rasu An Kashe Askarawa 6 da ‘Yan Sa-kai 4 A Zamfara 

Za a shafe kwanaki biyu ana gudanar da taron, bisa jigon “Ingiza karfin ci gaba, tare da inganta kyakkyawan ci gaban tattalin arzikin duniya”. Taron ya hallara wakilai daga manyan kamfanoni 86 na kasashe 21. A yayin taron, mahalarta na kasar Sin da na kasashen waje, za su gudanar da tarukan karawa juna sani 12, kan batutuwan da suka hada da manyan manufofi, da yin gyare-gyare, da kara yawan amfani da kayayyaki, da sabon karfin samar da hajoji da hidimomi masu karko, da fasahar AI.

Tun lokacin da aka kaddamar da dandalin tattauna raya kasa na kasar Sin a shekarar 2000, dandalin ya zama wata muhimmiyar gada da ta sa kaimi ga yaukaka tattaunawa, da hadin gwiwa tsakanin Sin da sauran kasashen duniya. (Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Arakci: Babu Wanda Zai Yi Tunanin Kawo Wa Iran Hari
  • Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Karfafa Gwiwar Kamfanonin Kasashen Duniya Da Su Fadada Zuba Jari A Sin 
  • NAJERIYA A YAU: Yadda watan Ramadana ke tasiri a harkokin kasuwanci
  • Firaministan Kasar Sin Ya Gana Da Sanata Steve Daines
  • An Bude Taron Shekara-Shekara Na Dandalin Tattauna Raya Kasa Na Sin Na 2025
  • Za’a Gudanar Taron Tattaunawa Tsakanin Rasha Ta Amurka A Karo Na Biyu 2 A Birnin Rayad na Kasar Saudiya
  • Jakadan Sin A Amurka: Mayar Da Karin Haraji Makami Kaikayi Ne Da Zai Koma Kan Mashekiya
  • Iran Ce Kasar Wacce Ta Fi Shigar Da Kayakin Kasuwanci Zuwa Kasar Afganistan A Shekarar Da Ta Gabata
  • Araghchi : Ya kamata Duniyar Musulmi ta dauki mataki mai karfi kan Isra’ila
  • Wang Yi: Kasar Sin Na Da Kwarin Gwiwa Kan Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Japan Da Koriya Ta Kudu