EFCC ta gargaɗi ciyamomi kan amfani da kuɗaɗen jama’a a Gombe
Published: 20th, February 2025 GMT
Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (EFCC), ta gargaɗi shugabannin ƙananan hukumomi da su guji almundahana tare da yin amfani da kuɗaɗen jama’a bisa gaskiya da adalci.
Shugaban EFCC, Mista Ola Olukoyede ne, ya bayyana haka yayin wani taro da aka shirya a Jihar Gombe kan ’yancin cin gashin kai na ƙananan hukumomi.
A cewarsa, samun ‘yancin cin gashin kai ba yana nufin cewa shugabannin ƙananan hukumomi ba za a iya hukunta su ba idan sun aikata ba daidai ba.
“Shugabannin ƙananan hukumomi ba su da kariya a tsarin mulkin ƙasa. Idan aka samu rashin gaskiya wajen sarrafa kuɗaɗen jama’a, dole ne a ɗauki mataki,” in ji Olukoyede.
Ya kuma bayyana cewa EFCC za ta ƙara tura jami’anta zuwa Jihar Gombe domin sanya ido kan yadda ake sarrafa kuɗaɗen ƙananan hukumomi.
Har ila yau, Olukoyede ya yaba wa hukuncin Kotun Ƙoli da ya bai wa ƙananan hukumomi damar samun cikakken iko kan kuɗaɗensu, inda ya ce hakan zai taimaka wajen inganta ayyukan ci gaba.
Sai dai ya nuna damuwa kan yiwuwar wasu su karkatar da kuɗaɗen da aka ware don ayyukan al’umma.
Ya yi kira ga shugabannin ƙananan hukumomi da su bi doka wajen sarrafa kuɗaɗen jama’a.
“Ku tabbatar da gaskiya a dukkanin ayyukanku, ku kuma san dokokin da suka shafi amfani da kuɗaɗen jama’a. Rashin sanin doka ba hujja ba ce,” ya gargaɗe su.
Taron, wanda aka yi wa take da “’Yancin Cin Gashin Kai na Ƙananan Hukumomi: Samar da Ci Gaba Mai Ɗorewa,” ya mayar da hankali ne kan yadda ake iya amfani da kuɗaɗen jama’a ta hanyoyin da za su amfanar da al’umma.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: gargaɗi Ƙananan Hukumomi amfani da kuɗaɗen jama a
এছাড়াও পড়ুন:
Ta kai ƙarar kamfanin jirgi da fasinja kan kukan yaro
Wata mata mai suna Jennifer Castro ta shigar da ƙarar kamfanin jiragen sama na GOL da wata fasinja a kotu bisa wani faifan bidiyo aka wallafa da yake nuna matar ta ki barin kujerarta da ke kusa da taga saboda wani yaro da yake kuka.
Matar ’yar ƙasar Brazil da ta ƙi barin kujerar kusa da taga saboda wani yaro mai kuka ta shigar da ƙara a kotu.
Tsohon kocin Super Eagles Christian Chukwu ya rasu An kashe Uba da ’ya’yansa biyu a ƙauyen FilatoJennifer Castro, mai shekara 29 na daukar matakin shari’a a kan kamfanin jiragin sama na GOl da kuma fasinjar da ta ɗauki bidiyonta a lokacin da lamarin ya faru.
Lamarin wanda aka yi ta yadawa ta intanet, ya janyo ce-ce-ku-ce a tsakanin jama’a.
A cewar jaridar The New York Post, Castro na tuhumar kamfanin jirgin da kuma matar da ya nadi musayar takaddamar da suka yi, inda ta nemi diyya kan halin kunci da barnar da lamarin ya haifar mata.
Ta bayyana cewa, matakin da ta ɗauka na shigar da ƙarar shi ne don hana afkuwar irin wannan abin kunya ga jama’a a nan gaba.
Al’amarin ya ja hankalin jama’a saboda yada lamarin a kafafen sada zumunta.
Da take bayani a kan shari’ar, Castro ta ki bayyana adadin diyyar da take nema.
Ta ce, tana son hana irin wannan tozarta jama’a da abin da ta kira fallasa ba tare da izini ba a nan gaba.
Hakan na zuwa ne bayan da aka bayar da rahoton cewa, a watan da ya gabata ta fara “tunanin” daukar matakin shari’a.
Castro ta bayyana cewa, “tun bayan faruwar wannan lamarin, rayuwata ta shiga wani yanayi da ban taba tunanin sa ba.”
“Abin da ya kamata ya kasance kawai jirgin zirgazirgar na yau da kullun ya sauya zuwa wani abun kunya, yana fallasa ni da rashin adalci da haifar da sakamakon da ya shafi rayuwata ta sirri da ta sana’a.
Ni ce ake so na yanke hukunci a kan takaddama da hasashen mutanen da ba su ma san cikakken labarin ba.”
Castro ta ce lamarin ya fara ne a lokacin da take hawa jirgi, sai ta hangi wani yaro a zaune a lambar kujerar da ya kamata ta zauna.
Tunda ta riga ta zabi wurin zama na kusa da taga, Castro ta yi tsammanin yaron zai koma wani wurin zaman na daban.
“Na jira shi yadda ya kamata, amma ya kwantar da kansa a wata kujerar, sannan sai na zauna a kujerata ,” in ji ta.
Lamarin ya ta’azzara lokacin da wata ta fara daukar bidiyon Castro ba tare da izininta ba.