EFCC ta gargaɗi ciyamomi kan amfani da kuɗaɗen jama’a a Gombe
Published: 20th, February 2025 GMT
Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (EFCC), ta gargaɗi shugabannin ƙananan hukumomi da su guji almundahana tare da yin amfani da kuɗaɗen jama’a bisa gaskiya da adalci.
Shugaban EFCC, Mista Ola Olukoyede ne, ya bayyana haka yayin wani taro da aka shirya a Jihar Gombe kan ’yancin cin gashin kai na ƙananan hukumomi.
A cewarsa, samun ‘yancin cin gashin kai ba yana nufin cewa shugabannin ƙananan hukumomi ba za a iya hukunta su ba idan sun aikata ba daidai ba.
“Shugabannin ƙananan hukumomi ba su da kariya a tsarin mulkin ƙasa. Idan aka samu rashin gaskiya wajen sarrafa kuɗaɗen jama’a, dole ne a ɗauki mataki,” in ji Olukoyede.
Ya kuma bayyana cewa EFCC za ta ƙara tura jami’anta zuwa Jihar Gombe domin sanya ido kan yadda ake sarrafa kuɗaɗen ƙananan hukumomi.
Har ila yau, Olukoyede ya yaba wa hukuncin Kotun Ƙoli da ya bai wa ƙananan hukumomi damar samun cikakken iko kan kuɗaɗensu, inda ya ce hakan zai taimaka wajen inganta ayyukan ci gaba.
Sai dai ya nuna damuwa kan yiwuwar wasu su karkatar da kuɗaɗen da aka ware don ayyukan al’umma.
Ya yi kira ga shugabannin ƙananan hukumomi da su bi doka wajen sarrafa kuɗaɗen jama’a.
“Ku tabbatar da gaskiya a dukkanin ayyukanku, ku kuma san dokokin da suka shafi amfani da kuɗaɗen jama’a. Rashin sanin doka ba hujja ba ce,” ya gargaɗe su.
Taron, wanda aka yi wa take da “’Yancin Cin Gashin Kai na Ƙananan Hukumomi: Samar da Ci Gaba Mai Ɗorewa,” ya mayar da hankali ne kan yadda ake iya amfani da kuɗaɗen jama’a ta hanyoyin da za su amfanar da al’umma.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: gargaɗi Ƙananan Hukumomi amfani da kuɗaɗen jama a
এছাড়াও পড়ুন:
Amurka Ta Bawa HKI Makami Mai Karfi, MK-87
Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhafa barakammu da sake saduwa a cikin shirimmu na duniyarmu a yau, shiri wanda yake kawo maku labarai masi muhimmanci a wannan makon wadanda suka hada da wadanda suka shafi siyasa tattalin arziki zamantakewa tsaro na sauransu, da fatana masu sauraro zasu kasance tare da mu a cikin shirimmu na yua.
//….. Madallah masu sauraro shirimmu na yau zia yi magana dangane da makamin bom masu suna MK-84 wanda kuma yake da Laba 2000 yake da katfin lalatawa da halaka mutane.
Shugaban kasar Amurka Donal Trump ya bayyanan bayan ya dare kan kujerar shugabancin kasar Amurka ya aikawa HKI manya-manyan boma-bomai masu nauyin ton guda ko wannan ake kira MK-84. Kara kashe Falasdinawa, `wannan kuma a fila ya kara bayyana cewa Amurka tana da hannun dumu-dumu a kissan Al-ummar Falasdinu a gaza.
Har’ila yau wannan ya nuna cewa HKI tana son ta maye gurbin makaman da ta rasa a yakin da ta gwabza fa Falasdnawa na kimani watanni 15 a Gaza, saboda a ranar lahadin da ta gabata ce sojoji HKI suka bada sanarwan cewa sun karmu makamai samfurin MK84-84 har guda 1,800 daga kasar Amurka wadanda shugaba Trump ya sanyawa hannu watan da ya gabata.
Sun isa tashar jiragen ruwa na Ashdod kuma tuni an kaisu sansanin jiragen saman yakin da ya dace.
Ministan yaki na HKI Isarel Katz ya godewa sabon shugaban kasar Amurka Donal Trump saboda goyon bayan da yake bawa HKI kan Falasdinawa. Musamman sabbon boma boman da ya basu wanda zai tabbatar da ikon HKI kan falasdinawa.
Ministan yakin ya kara da cewa tun bayan fara yaki a Gaza a ranar 7 ga watan Octoban shekara ta 2023 HKI ta karbi taimakon makamai ton 76,000 mafi yawansu daga kasar Amurka. Ministan ya kara cewa wasu makaman sun shigo HKI ta jiragen sama 678 sannan sauran kuma ta jiragen ruwa 129.
Ya ce shugaba Biden ya aikawa HKI boma-boman MK84 a cikin watanni 7 na farko a yankin, amma cikin watan mayun shekarar da ta gabata ya dakatar. Yayi haka ne don takurawar da kungiyoyi kare hakkin bil’adama a duniya. Wadanda suka damu da irin kissan kiyashin da HKI take yi a Gaza.
Wasu majiyoyi sun bayyana cewa Biden ya dakatar ne saboda zabubbuka masu zuwa a cikin watan Nuwamba na shekarar da ta gabata, yana neman kuri’un Amurkawa wadanda suka damu da yadda HKI take nika Falasdinawa da wadannan boma-boman.
Sai dai duk da haka gwamnatin Biden bada dakatar da bawa HKI makamai da kuma tallafi ba duk tare da cewa bai sami nasara a zaben ba.
Bayan shigarsa white House shugaba Trump ya dage takunkuman bawa HKI makaman na MK87 a ranar 26 ga watan Jenerun shekara ta 20205.
Kasashen duniya da dama sun yi allawadai da shugaban Trump saboda dage wannan takunkumin, saboda akwai tsoron Natanyahu zai yi watsi da yarjeniyar tsagaita budewa Juna wuta a Gaza, ya ci gaba da kissan kiyashin da yakewa mutanen na Gaza.
Amma menen bom mai suna MK84 wanda ake magana a kansa. Masana suna cewa boma-bomai MK87 dai suna boma bomai mafi karfi wadanda gwamnatin kasar Amurka ta mallaka, kuma akwai wadanda ta fara kerasu tana kuma kara karfinsu kadan –kadan har ya kai MK87.
Kafin haka dai Amurka ta fara kera makami ko boma bomai MK 80, sannan MK 81, sannan 82, sai 83.
Baoma-baman MK 87 dai sune mafi karfi daga cikinsu, wanda yake da karfinb fashewa da kuma lalata duk abinda aka jefashi a kai. Masana sun kara da cewa nauyin Bom MK87 ya kai pound 2000 ko kuma kilogram 907. An cikashi da sinadarin TNT da garin alumiium. Har’ila yau wani bangare na makaman na MK87, an yi shi da karfe, wanda kuma shi kasha 45% na dukkan nauyin makamin. Wannan kuma don samar da fashewa mai karfi idan ya fada kan wani abu.
Sannan ana amfani da jiragen yaki ne don jefa boma-boman MK87 kuma idan ya isa kan abinda ake nufi da shi sai yayi rami babban kafin ya fashi don tabbatar da cewa ya lalata wurin da aka jefa shi gaba daya. Idan ginie to ginin gaba daya zai fada kuma kuma rugurguje.
Masanan sun kara da cewa boma-boman MK87 suna iya huda konkere mai fadin cm 60-105, sannan zai tona kasa mai zurfin mita biyar kafin ya fashe. Idan kasar mai lauci ne kuma yana iya fin haka.
Sannan jiragen yakin da suke iya daukar irin wadannan boma boman sun hada da A-10, B-1B, B-52, F-4, F-15, F-16, F-111 da kuma F-117. Har’ila yau jiragen yakin kasashen Turkiyya da Saudiya da HKI suna da karfin daukar makaman na MK87. Gwamnatin kasar Amurka ta fara amfani da irin wadannan makamai ne a shekaru 1970 a yakin Vetnam, sannan ta yi amfani da su a yakin Iraq, Yugoslavia da Afghanistan, hakama gwamnatin saudiya ta yi amfani da irin wadannan boma bomai a kan mutanen yemen. Sai kuma HKI ta yi amfani da irin wadannan boma bomai kan Falasdinawa a gaza da kuma mutanen kasar Lebanon a yakin tufanul Aksa.
Wadannan gwamnatoci dai suna amfani da wadannan boma bomai ne a mafi yawan lokuta kan gidajen mutanen inda za’a suke kashe mutanen fararen hula masu yawa.
HKI dai ta sha amfani da makaman MK84 kan falasdinawa ton shekara 1982 zuwa gaba, tare da amfani da jiragen yaki samfurin F16 da FF 15.
Banda haka HKI tana da makamai masu karfi fiye da MK87, kuma sun yi amfani da su kan falasdinawa ya fi a irga. Sun kama rusa gidajensu a kansu tare da amfani da irinsu.
Jiragen yakin HKI sun yi amfani da MK84 a kan cinkoson falasdinawa da kuma muatnen kasar Lebanon a garin Qana inda suka kashe yara 17 da manyan mutane 12 a birnin Beirut a shekara ta shekara ta 2006 a lokacin da ta fafata da kungiyar Hizbullah.
Sai dai duk tare da wadannan boma bimai ta kara samun nasara a kan kungioyar Hizbullah a yakin na kwanaki 33. Sai dai ta kashe fararen hula 1,400 tare da amfani da wadannan bomai boamai.
Sai dai duk tare da makaman da take da su, daga cikin har da MK87 wannan bai bata nasara a kan makiyanta ba.
Mun san cewa sojojin HKI sun yi amfani da makamai daban daban a yake yake daban daban da suka shiga da falasdinawa a Gaza ko kuma hizbullah a Lebanon amma basu sami nasara a dukkan yake –yaken ba.
Sannan ya yakinta na karshe na watanni 15 ma ta kasa cimma manufofinta a yakin gaba daya. Bata kwace gaza ba, bata bata kwace .
Haka kuma a yakin shekara ta 2023 ta kasa shiga kasar Lebanon.
Wani abin lura a yankin 7 ga watan octoba na shekara ta 2023, gwamnatin HKI ta kasa cimma manufofinta a Gaza da kuma kasar Lebanon, duk tare da barnan da suka yiwa shuwagabannin kungiyar Hizbullah da kuma Hamas.
Wannan yana tabbatar mana cewa yawan makamai da kuma sojoji ba sune suke bada nasara a yaki ba.
Sai dai sadaukawa, da nuna jarunta, har ‘ila da taimakon All..ga musulmi shi ne yake bada nasara kuma yake rusa makiya.
A shekara ta 2023 ko kuma a yakin 7 ga watan Octoba, har zuwa karshen yakin a ranar 19 ga watan Jenerun shekara ta 2025. Sojojin HKI sun rusa fiye da kasha 80% na zirin gaza. Amma kuma ta kasa samun kwato yahudawan da suke tsare a hannun Hamas, ta kuma kasa mamayar kasar Lebanon. Sojojin HKI basu taba rasa sojoji da fararen hula a yaki guda kamar yadda suka rasa a yankin Tufanul Aksa ba.
Sannan wani abin mamaki shi ne, makaman MK87 ba sabbon makami ne ga HKI ta taba amfani da sun a watanni 7 a farkon yakin tufanul Aksa, kamar yadda muka bayyana, kafin shugaban biden ya hanasu, don haka idan Trump ya mayar masu, wannan bay a nuna makaman zasu yi aiki fiye da yadda suka yi aiki a baya ba.
Masan suna ganin yakin Tufanul Aksa ya tabbatar da cewa HKI ba zata sake samun nasara a kan kungiyar Hizbullah ta kasar Lebanon ko kuma kungiyoyin Falasdinawa a Gaza ba, saboada sun yi amfani da dukkan makamai masu karfinda Amurka take da su amma sun kasa samun nasara a kan makiyanta. Don haka babu bambanci idan har sun yi amfani da makaman da suka kai karfin wadanda suka yi amfani da sub a ko wadanda suka fisu karfi.
Sannan wadannan kungiyoyi a gaza ko a kasar Leabanon sun sami makaman da zasu iya cillasu a kan yahudawa da cibiyoyin makamai na HKI a cikin haramtacciyar kasar, kuma ya tabbatar cewa garkuwan makaman da suka mallaka basa iya kakkabosu gaba daya, ya nuna cewa zaman lafiya ta kara a HKI Kenan.
Idan masu sauraro zasu tuna makamai masu linzami masu karfi wadanda suke kaiwa kan birnin Haifa da Tel Aviv ne suka tilastawa HKI neman tsagauita wuta da HKI a yankin na baya bayan nan.
Matukar wadannan makaman suna hannun kungiyar Hizbullah HKI ba zata kuskura ta farfa yaki da Hizbullah ba.
Shi yasa a halin yanzu tske son haka kai da wadanda suke tare da su a cikin gwamnatin kasar Lebanon ko kuma ma’aikatar leken asiransu don ganin sun raba hizbullah da makamanta , a sannan zasu sake famata da yaki idan har zuwa iya kwace makaman na kungiyar.