HausaTv:
2025-02-22@06:26:21 GMT

Saudiyya ta Gayyaci Kasashen Larabawa Kan Batun Kan Batun Gaza

Published: 20th, February 2025 GMT

Saudiyya ta kira shugabannin kasashen Larabawa na yankin Gulf da kuma Masar da Jordan a wani taron domin tattauna batun Gaza.

Yarima mai jiran gado na Saudiyya, Mohammed bin Salman, ne ya gayyaci shugabannin a taron na gobe Juma’a, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Saudiyyar SPA ya ruwaito.

Kasashen Larabawa sun yi alkawarin yin aiki a kan wani shiri na bayan yakin Gaza da kuma  sake gina Zirin a wani mataki na tunkarar shawarar shugaban Amurka Donald Trump na sake gina yankin da mayar da shi wurin shakatawa na gabar tekun kasa da kasa bayan korar mutanen Gaza zuwa wasu wurare.

Saudiyya ta ce taron na ranar Juma’a zai kasance ba na hukuma ba kuma za a yi shi ne cikin “tsarin dangantakar ‘yan’uwantaka da ke hada shugabannin,” in ji kamfanin SPA.

A cewar labarin, dangane da matakin da kasashen Larabawa suka dauka na hadin gwiwa da kuma shawarwarin da aka fitar dangane da shi, zai kasance cikin ajandar taron gaggawa na kasashen Larabawa da za a yi a Masar,” in ji SPA, yayin da yake magana kan shirin taron gaggawa na kasashen Larabawa da za a yi a ranar 4 ga watan Maris mai zuwa domin tattauna rikicin Isra’ila da Falasdinu.

Shi dai shugaban Amurka D.Trump ya yi kira ga kasashen Masar da Jordan su karbi Falasdinawa da ba su wajen zama bayan fitar da su daga Gaza, shawarar da kasashen suka yi fatali da ita.

Kasashen duniya da dama sun soki matakin na Trump, suna masu danganta shi da raba Falasdinawa da kasarsu ta gado.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasashen Larabawa

এছাড়াও পড়ুন:

Trump Yana Son Ganin Bayan Shugaban Kasar Ukraine Volodimir Zelezky Daga Kujerar Shugabancin Kasarsa

A dai-dai lokacinda shugaban kasar Amurka Donal Trump ya bayyana a fili kan cewa baya son nganin tokwaransa na kasar Ukraine Volodimir Zelesky kan kujerar shugabancin kasarsa. Al-amura suna kara tabarbarewa a Kiev.

Jaridar Economist ta kasar Burtaniya ta bayyana cewa al-amarin ya bayyana kiri-kiri ne a lokacinda shugaban kasar Amurka ya zanta ta wayar tarho da shugaban kasar Rasha Vladimi Putin. Sannan aka gudanar da taro na farko tsakanin Amurka da Rasha a birnin riyad na kasar Saudiya ba tare da an gayyaci Zelesky ba haka ma, babu wani Jami’in tarayyar Turai da aka gayyata.

Jaridar ta nakalto wani babban jami’in gwamnati a Kiev yana cewa tun lokacinda suka fahinci cewa Trump baya son a ci gaba da yaki a Ukraine, sannan baya son shugaba Zeleski sun san haka zai faru.

Banda haka, Trump ya bayyana cewa Amurka ta kashe dalar Amurka miliyon 360 kan yakin da ta tabbatar da cewa Ukrain ba zata sami nasara ba. Banda wannan ya ji ta bakin Zeleski kansa kan cewa an sace rabin kudaden da Amurka ta bata.  A halin yanzu dai Trump ya bukaci a gudanar da zabe a kasar Ukraine, don ya tabbatar da cewa Zelesky bai da magoya baya da yawa. A cikin watan Fabrairun da mukr ciki ne yaki tsakanin Ukraine da Rasha yake cika shekaru 3 da fara shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Kudiri Anniyar Karfafa Alakarta Da Kasashen Afirka
  • Shugabannin Kasashen Larabawa Sun Tattauna Kan Batun Gaza Da Yankin
  • Kasar Sin Ta Bukaci G20 Ta Zama Karfin Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali A Duniya
  • Najeriya ta taɓarɓare bayan mulkin IBB – Obi
  • Trump Yana Son Ganin Bayan Shugaban Kasar Ukraine Volodimir Zelezky Daga Kujerar Shugabancin Kasarsa
  • Kungiyoyin Falasdinawa A Gaza Sun Bukaci Yin Taron Musamman Domin Dakile Batun Tilasa Wa Mutanen Gaza Yin Hijira
  •  Jagora: Siyasar Kasar  Iran  Ta Ginu Ne Akan Kyautata Alaka Da Kasashen Makwabta
  • Ukraine ce mai laifi a yaƙin da ta ke yi da Rasha — Trump
  • Kasashen Rasha Da Amurka Sun Kuduri Anniyar Kawo Karshen Yaki A Ukraine