Da yake jawabi ga manema labarai a Abuja a ranar Laraba, Ogbugo Ukoha, Babban Darakta a sashen rarraba mai tare da adanawa na NMDPRA, ya ce matakin ya biyo bayan karuwar firgicin hadurran da ke tattare da manyan motocin dakon man.

 

“Kwamitin fasaha na masu ruwa da tsaki ya gana a yau don cimma wasu muhimman kudurori guda 10 da nufin rage karuwar yawan hadurran tankokin mai da ke janyo asarar rayuka,” in ji Ukoha.

 

An cimma wannan matsaya ne bayan tattaunawa da manyan masu ruwa da tsaki da suka hada da DSS, hukumar kashe gobara ta tarayya, hukumar kiyaye hadurra ta kasa (FRSC), kungiyar masu sufurin mota ta kasa (NARTO), kungiyar ma’aikatan man fetur da iskar gas ta kasa (NUPENG), hukumar tabbatar da ingancin kayayyaki ta kasa (SON), DAPPRAMAN da NDPRAMAN.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Babban Daraktan Hukumar IAEA, Zai Ziyarci Iran ranar Laraba

Babban daraktan hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya  zai ziyarci Tehran a ranar Laraba mai zuwa.

Ziyarar ta Grossi na zuwa ne gabanin sabuwar tattaunawar da za’ayi tsakanin Iran da Amurka a ranar Asabar mai zuwa kan batun shirin nukiliyar Iran na zaman lafiya.

Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Iran mai kula da harkokin kasa da kasa Kazem Gharibabadi ya ce shugaban hukumar ta IAEA Rafael Grossi zai ziyarci Tehran a ranar Laraba.  

Gharibabadi ya bayyana cewa, babban daraktan hukumar ta IAEA, zai gana da ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi da shugaban hukumar makamashin nukiliya ta Iran (AEOI) Mohammad Eslami.

Ya kara da cewa “ziyarar na cikin tsarin ci gaba da hulda da hadin gwiwa tsakanin bangarorin biyu.”

Ziyarar ta shugaban hukumar ta IAEA za ta zo ne a daidai lokacin da Iran da Amurka ke shirin gudanar da tattaunawar ta biyu, wanda Oman ta shiga tsakani a ranar Asabar data gabata.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Babban Daraktan Hukumar IAEA, Zai Ziyarci Iran ranar Laraba
  •  Tsoffin Ma’aikatan Hukumar Leken Asiri HKI  Mosad Sun Shiga Cikin Masu Kiran A Kawo Karshen Yaki Da Gaza
  • An kama kwayoyin N300m da mutane 650 a Kano
  • An kama miyagun kwayoyin N300m da mutane 650 a Kano
  • A daina cutar ’yan Najeriya ta hanyar rabon kayan tallafi
  • Bam Ya Halaka Mutum 8, Ya Jikkata Wasu Da Dama A Borno
  • Jama’ar Gabon sun kada kuri’a a zaben shugaban kasa, na farko bayan mulkin zuri’ar Bongo
  • ‘Tell Your Papa’: NBC ta haramta amfani da waƙar da ke sukar Tinubu
  • Atiku ya jagoranci manyan ’yan siyasa sun ziyarci Buhari
  • Basukan Da Nijeriya Ke Biya Sun Karu Zuwa Naira Tiriliyan 13