Ɗaliba ta rasu yayin da gini ya rufta a GGTC Potiskum
Published: 20th, February 2025 GMT
Wani ginin ajujuwa a Kwalejin ’Yan Mata ta Kimiyya da Fasaha (GGTC) Potiskum ya rufta, inda daliba ɗaya ta rasu kuma wasu da dama suka jikkata.
Majiyoyi sun bayyana cewa lamarin ya faru ne yayin da ɗalibai ke tsaka da karatu.
An rufe Jami’ar Kogi saboda zanga-zangar ɗalibai EFCC ta gargaɗi ciyamomi kan amfani da kuɗaɗen jama’a a GombeGini ya faɗa kansu ne ba zato ba tsammani, lamarin ya haddasa mummunan tashin hankali tare da jefa ɗalibai da dama cikin baraguzan gini.
Bayan aukuwar lamarin, an yi gaggawar ceto ɗaliban, inda aka garzaya da su zuwa Asibitin Ƙwararru na Potiskum domin ba su kulawa.
Duk da an samu nasarar ceto da dama daga cikinsu, wata ɗaliba ta rasa ranta sakamakon raunukan da ta samu.
Tuni Kwamishinan Ilimi a matakin Farko da Sakandare, Farfesa Abba Idris Adam, tare da Sakataren Zartarwa na Hukumar Kimiyya da Fasaha ta Jihar Yobe, Dokta Dauda Atiyaye, suka ziyarci wajen da lamarin ya faru, da kuma asibitin da ake kula da ɗaliban da suka jikkata.
Har yanzu ba a bayyana abin da ya yi sanadin rushewar ginin ba.
Amma hukumomi na ci gaba da bincike don gano haƙiƙanin dalilin aukuwar iftila’in.
Garin Potiskum na da nisan kilomita 100 daga Damaturu, Babban Birnin Jihar Yobe.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: yan mata Ɗaliba Ɗalibai karatu rasuwa
এছাড়াও পড়ুন:
An shiga ruɗani yayin da Sanusi II da Bayero ke shirin hawan salla a Kano
Al’ummar Jihar Kano, sun shiga shida ruɗani yayin da rikicin Masarautar jihar, ya ɗauki wani sabon salo game da shirin gudanar da bikin hawan salla.
Tsagin sarakunan jihar na 15 da na 16, wato Muhammadu Sanusi II da Aminu Ado Bayero, sun shirya gudanar da hawan salla duk da shari’ar da ke gudana kan rikicin masarautar.
Matasa sun kashe yaron da suka yi garkuwa da shi a Bauchi Mata sun ƙwace kasuwancin kayan lambu a GombeLamarin ya ɗauki sabon salo ne, bayan wata wasiƙa daga Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero, ya fitar kan shirinsa na yin hawan salla a bana.
Wasiƙar, wacce sakataren Sarkin, Abdullahi Haruna Kwaru, ya sanya wa hannu, an aike wa Kwamishinan ’Yan Sandan Kano, inda ya bayyana shirinsa na gudanar da hawan salla.
Daga cikin hawan da ya bayyana cewar zai yi akwai Hawan Daushe, da Hawan Nassarawa a ranakun 2 da 3 ga watan Shawwal 1446 bayan hijira.
Wannan na zuwa ne bayan Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya umarci Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, da ya fara shirin gudanar da hawan salla.
A cikin wasiƙarsa, Aminu Ado, ya ce wannan hawan na da muhimmanci a gare shi saboda zai cika shekarj biyar da zama sarki.
An jima ba a gudanar da bikin hawan salla ba a Kano saboda fargabar abin da ka iya faruwa tsakanin mabiyan sarakunan biyu.
Rikicin ya fara ne bayan da tsohon gwamnan jihar, Abdullahi Umar Ganduje ya tuɓe Sanusi II daga sarauta, tare da naɗa Aminu Ado a matsayin Sarkin Kano.
Sai dai a shekarar 2024, Majalisar Dokokin Kano, ta sake sauya dokar masarautar tare da rushe dukkannin masarautu biyar da Ganduje ya ƙirƙira, tare da mayar da Sanusi II a matsayin Sarki.
Wannan ya janyo ce-ce-ku-ce da tashin hankali a jihar, lamarin da ya sanya tsagin Aminu Ado tafiya kotu.
Kotu ta yanke hukuncin cewa komai ya ci gaba da zama a yadda yake har zuwa lokacin da Kotun Ƙoli za ta yanke hukuncin ƙarshe, lamarin da ya sa dukkanin ɓangarorin biyu ke iƙirarin suna da iko a kan sarautar.
Har yanzu, gwamnatin Kano da Sanusi II ba su ce komai ba kan wasiƙar da Aminu Ado, ya aike wa ’yan sanda, kuma har yanzu ba a ji ta bakin rundunar ’yan sandan jihar ba.
Sai dai, jama’a na nuna damuwa kan abin da ka iya faruwa.
Malam Haladu Bello, wani dattijo mai shekaru 78 a duniya, ya bayyana damuwarsa kan cewa lamarin zai iya haifar da rikici.
“Na sha ganin hawan salla mai ƙyatarwa da kuma wanda ke da matsaloli, amma wannan yana da ban tsoro.
“Abin takaici ne yadda shugabanninmu ke watsi da hatsarin da jama’a ke fuskanta.”
Wani matashi mai shekaru 30, Alhaji Usman Shehu, ya bayyana cewa wannan rikicin cikin gida ne, ba wai abu ne da zai sa mutane cikin fargaba ba.
Ya ce: “Kullum cikin fargabar abin da zai biyo baya muke. Wannan ba daidai ba ne. A bar mu, mu more al’adunmu cikin zaman lafiya.”
Yayin da bikin salla ke ƙara ƙaratowa, al’ummar Kano na ci gaba da fargabar abin da ka iya faruwa idan duka sarakunan biyu suka ci gaba da shirinsu na gudanar da hawan salla.