Gwamna Umar Namadi na jihar Jigawa ya kaddamar da shirin Da’awah na mata a hukumance, domin karfafawa mata ilimin addinin musulunci, da karfafa alakar iyali, da kyautata rayuwa a tsakanin.

Da yake jawabi a wajen bikin a Dutse, Gwamna Namadi ya jaddada muhimmiyar rawar da mata ke takawa wajen tsara tarbiyar al’umma da kyawawan dabi’u.

“Kamar yadda aka sani, kusan rabin al’ummar jihar Jigawa mata ne, wadanda suka hada da iyayenmu, da ‘ya’yanmu, wanda hakan ya sa ya zama wajibi a kara zage dantse domin kula da addini da kuma tarbiyyarsu”.

Malam Umar Namadi ya jaddada wajibcin addini da ya rataya a wuyan maza na tallafa wa mata da bi da su hanyar shiriya, inda ya bukaci maza da su kyautata mata kamar yadda addini ya tanadar.

Ya kuma yabawa ma’aikatar harkokin mata da ci gaban al’umma ta jiha bisa jajircewarta wajen samun nasarar shirin, tare da yabawa babbar rawar da uwargidansa Hajiya Hadiza Umar Namadi ta taka wajen daukar nauyin shirin.

Namadi ya kuma yabawa Majalisar Malamai ta Jiha da dukkan masu ruwa da tsaki, bisa kokarin da suka yi wajen bunkasa tsarin da samar kayan aikin.

“Na yaba da kokari da sadaukarwar da kuka nuna wajen tabbatar da samun nasarar wannan shiri, Allah ya karbi dukkan gudunmawar da kuka bayar a matsayin Sadaqatul Jariyya.”

Ya kuma bukaci dukkan mahalarta taron da su rungumi shirin da zuciya daya, tare da jaddada muhimmancin ikhlasi, da kyawawan halaye, da hakuri da ayyukan Da’awah, tare da karfafa musu gwiwa da su rungumi koyarwar Alkur’ani mai girma.

Gwamnan ya kuma jaddada kudirin gwamnatinsa na tallafawa ci gaban mata, tare da yin kira ga shugabannin addini da na al’umma da su ci gaba da gudanar da shirin a dukkan kananan hukumomin jihar.

Gidan Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, shirin wanda hadin gwiwa ne tsakanin Gwamnatin Jihar Jigawa, Majalisar Malamai ta Jiha, da sauran shugabannin addini da na al’umma, na neman ilmantar da mata kan koyarwar addinin Musulunci, da inganta rawar da suke takawa wajen ci gaban iyali da ci gaban al’umma tare da samar da zaman lafiya, da kyautatawa da mutunta juna.

A karkashin shirin an zabo mata 574 daga sassa daban-daban na jihar.

 

Usman Muhammad Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Da awah Jigawa jihar Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Zaɓen ƙananan hukumomin Osun na nan daram – Gwamna Adeleke

Gwamnan Jihar Osun, Ademola Adeleke ya ce ya sha alwashin cewa zaɓen ƙananan hukumomin da za a yi a jihar a gobe Asabar zai gudana kamar yadda aka tsara.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a matsayin martani kan shawarar da ministan shari’a na Najeriya, Lateef Fagbemi, wanda ya buƙaci gwamnatin jihar ta dakatar da yunƙurin yin sabon zaɓen ƙananan hukumomi.

Najeriya ta taɓarɓare bayan mulkin IBB – Peter Obi An ƙwace miliyoyin daloli, gidajen da ke da alaƙa da Emefiele

A cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Alhamis, Ministan ya ce kotu ta dawo da zaɓaɓɓun shugabannin ƙananan hukumomin da aka zaɓa a ƙarƙashin tsohon Gwamna Gboyega Oyetola, amma ta tsige su ta hanyar umarnin zartarwa da gwamnan ya yi.

Fagbemi ya ce ba bisa ƙa’ida ba ne a gudanar da zaɓen ƙananan hukumomi a Osun kafin watan Oktoba lokacin da wa’adin shugabanni da kansilolin da aka zaɓa a Jam’iyyar APC zai ƙare.

Sai dai a wata sanarwa da kakakin Gwamnan, Olawale Rasheed ya fitar, gwamnan ya ce mutanen jihar a shirye suke tsaf kuma babu gudu babu ja da baya kan gudanar da zaɓen.

Ya bayyana haka ne a lokacin da yake karɓar rukunin gamayyar ƙungiyoyin farar hula da suka je jihar domin sanya ido kan zaɓen ƙananan hukumomi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zaɓen ƙananan hukumomin Osun na nan daram – Gwamna Adeleke
  • Tsarin Fansho Na Jihar Jigawa Ya Yi Wa Sauran Jihohi Zarra- Premium Pension
  • Malamai Na Karbar Horo Akan Shirin Ilimin Mata Na AGILE a Jigawa
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kaddamar Da Rangadi A Karamar Hukumar Jahun
  • UNICEF Ya Jinjinawa Jihar Jigawa
  • Shirin Rigakafin Cututtuka Na UNICEF/GAVI Ya Sami Cikakken Hadin Kan Gwamnatin Jihar Jigawa
  • NAJERIYA A YAU: Tanadin Dokar Kasa Kan Kirkirar Gwamnatin Bibiya A Kano
  • Matasan Jihar Jigawa Sun Karrama Gwamna Umar Namadi
  • Gwamnatin Gombe ta horar da makiyaya kan sabbin hanyoyin kiwo