Gwamna Namadi Ya Kaddamar Da Shirin Da’awah Na Mata A Jihar Jigawa
Published: 21st, February 2025 GMT
Gwamna Umar Namadi na jihar Jigawa ya kaddamar da shirin Da’awah na mata a hukumance, domin karfafawa mata ilimin addinin musulunci, da karfafa alakar iyali, da kyautata rayuwa a tsakanin.
Da yake jawabi a wajen bikin a Dutse, Gwamna Namadi ya jaddada muhimmiyar rawar da mata ke takawa wajen tsara tarbiyar al’umma da kyawawan dabi’u.
“Kamar yadda aka sani, kusan rabin al’ummar jihar Jigawa mata ne, wadanda suka hada da iyayenmu, da ‘ya’yanmu, wanda hakan ya sa ya zama wajibi a kara zage dantse domin kula da addini da kuma tarbiyyarsu”.
Malam Umar Namadi ya jaddada wajibcin addini da ya rataya a wuyan maza na tallafa wa mata da bi da su hanyar shiriya, inda ya bukaci maza da su kyautata mata kamar yadda addini ya tanadar.
Ya kuma yabawa ma’aikatar harkokin mata da ci gaban al’umma ta jiha bisa jajircewarta wajen samun nasarar shirin, tare da yabawa babbar rawar da uwargidansa Hajiya Hadiza Umar Namadi ta taka wajen daukar nauyin shirin.
Namadi ya kuma yabawa Majalisar Malamai ta Jiha da dukkan masu ruwa da tsaki, bisa kokarin da suka yi wajen bunkasa tsarin da samar kayan aikin.
“Na yaba da kokari da sadaukarwar da kuka nuna wajen tabbatar da samun nasarar wannan shiri, Allah ya karbi dukkan gudunmawar da kuka bayar a matsayin Sadaqatul Jariyya.”
Ya kuma bukaci dukkan mahalarta taron da su rungumi shirin da zuciya daya, tare da jaddada muhimmancin ikhlasi, da kyawawan halaye, da hakuri da ayyukan Da’awah, tare da karfafa musu gwiwa da su rungumi koyarwar Alkur’ani mai girma.
Gwamnan ya kuma jaddada kudirin gwamnatinsa na tallafawa ci gaban mata, tare da yin kira ga shugabannin addini da na al’umma da su ci gaba da gudanar da shirin a dukkan kananan hukumomin jihar.
Gidan Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, shirin wanda hadin gwiwa ne tsakanin Gwamnatin Jihar Jigawa, Majalisar Malamai ta Jiha, da sauran shugabannin addini da na al’umma, na neman ilmantar da mata kan koyarwar addinin Musulunci, da inganta rawar da suke takawa wajen ci gaban iyali da ci gaban al’umma tare da samar da zaman lafiya, da kyautatawa da mutunta juna.
A karkashin shirin an zabo mata 574 daga sassa daban-daban na jihar.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Da awah Jigawa jihar Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
NUJ Ta Bada Tallafin Azumi Ga Iyalan Mambobinta Da Suka Rasu A Jihar Kebbi
Kungiyar ‘Yan Jaridu ta Najeriya (NUJ) reshen Jihar Kebbi ta raba kayan abinci da kudi ga iyalan mambobinta da suka rasu a lokacin da suke kan aikin jarida, a matsayin kyautar azumin Ramadan.
Da yake jawabi a wajen taron, Shugaban Kungiyar na Jiha, Kwamared Bello Sarki Abubakar, ya ce suna gudanar da wannan shiri a duk shekara, tun bayan kaddamar da shi da tsohon shugaban kungiyar na jiha Alhaji Aliyu Jajirma ya yi, domin faranta ran iyalan abokan aikinsu da suka rasu.
Kwamared Sarki Abubakar ya bayyana cewa dukkan shugabannin kungiyar da suka gabata sun tabbatar da ci gaba da gudanar da wannan shiri a duk lokacin azumin Ramadan domin rage wa iyalan mamatan radadin wahalhalun rayu.
Ya sanar da cewa kowane iyali daga cikin iyalan mambobi 21 da suka rasu za su karɓi buhun shinkafa mai nauyin kilogiram 25 da kuma naira dubu goma.
Yayin da yake gode wa Gwamnatin Jihar Kebbi karkashin jagorancin Kwamared Nasiru Idris saboda goyon bayan da take bai wa kungiyar, Kwamared Sarki ya yaba da ayyukan ci gaba da Gwamna Nasir Idris ya aiwatar a cikin shekaru biyu da suka gabata domin inganta rayuwar al’ummar jihar.
Kwamishinan Watsa Labarai da Al’adu na Jihar Kebbi, Alhaji Yakubu Ahmed BK, yayin da yake yaba wa shugabancin kungiyar saboda tallafin da ta bai wa iyalan mamatan, ya tabbatar wa kungiyar cewa Gwamnatin jihar za ta ci gaba da fifita jin daɗin ‘yan jarida a jihar.
Haka kuma, ya yi alkawarin yin duk mai yiwuwa don tabbatar da cewa badi an gudanar da wannan taro cikin gagarumin shiri domin faranta wa iyalan mamatan rai.
A madadin wadanda suka ci gajiyar tallafin, daya daga cikin matan wadanda suka rasu, Hajiya Hadiza Abdullahi, ta gode wa kungiyar saboda tunawa da su bayan rasuwar mazajensu.
Daga Abdullahi Tukur