Shugaba Tinubu Ya Yaba Da Gudunmawar Da IBB Ya Bayar Yayin Mulkinsa
Published: 21st, February 2025 GMT
Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yabawa tsohon shugaban kasa na mulkin soja, Janar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB) bisa irin gudunmawar da ya bayar ga ci gaban Najeriya.
Shugaban kasar a bayyana hakan ne a lokacin kaddamar da tallafin, tarihin rayuwar Janar Babangida da gwagwarmayarsa yayin aiki, wanda aka gudanar a Abuja.
A yayin da yake jawabi a matsayin babban bako na musamman, Tinubu ya bayyana ga irin jagoranci Babangida a yayin mulkinsa, wanda ya ce ya abin koyi ne ga kowa.
Ya kuma yaba da rawar da IBB ya taka wajen kafa sabbin bankuna na zamani, wanda ya kawo kyakkyawa sauyi a fannin hada-hadar kudi na Najeriya.
Tinubu ya kuma yabawa manufofin Babangida da salon shugabancinsa da suka yi tasiri a nasa salon siyasar, inda ya jaddada kokarin Babangida wajen inganta dimokuradiyya da kawo sauyi a tattalin arziki.
Tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo, wanda ya gabatar da jawabi mai ma’ana, ya yabawa Babangida bisa rubuta tarihin rayuwarsa da irin gudunmawar da ya bayar a tarihin Najeriya.
Obasanjo ya jaddada mahimmancin adana bayanan tarihi don taimakawa al’umma masu zuwa, domin gano kura-kurai da suka gabata, da yadda za a gyara, da kuma taimako wajen gina kasa.
A wani muhimmin jawabi, tsohon shugaban kasar Ghana, Nana Akufo-Addo, ya yaba da shugabancin Babangida a Najeriya, inda ya jinjina gudunmawar da ya bayar wajen tabbatar da dimokuradiyya a yammacin Afirka.
Kazalika shi ma tsohon shugaban kasa Yakubu Gowon ya tuna irin jajircewa da Babangida ya nuna a lokacin da yake aikin soja.
Ya lura da biyayyar Babangida da kokarin daidaita gwamnatin Najeriya a lokacin yunkurin juyin mulki da sauran kalubalen siyasa.
A nasa jawabin, tsohon mataimakin shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo ya yi nazari mai zurfi game da littafin, inda ya yaba da abin da ya kunsa, da kuma yadda Babangida ya karrama wadanda suka yi aiki tare da shi.
A nasa jawabin, Babangida ya bayyana godiya ga dukkan wadanda suka halarci taron da suka hada da gwamnoni, da sanatoci, da sarakunan gargajiya, da wakilan kamfanoni masu zaman kansu.
Ya yi waiwaye kan kalubale da sadaukarwar da aka yi a lokacin gwamnatinsa, ya kuma bayyana irin matsalolin da al’ummar Najeriya ke fuskanta.
Babangida ya fito karara ya yi magana kan soke zaben shugaban kasa da aka yi a ranar 12 ga watan Yunin 1993, inda ya dauki cikakken alhakin wannan mataki.
Ya bayyana cewa an dauki dukkan matakan ne da domin gujewa tashin hankali, da kuma tabbatar da zaman lafiyar Najeriya.
Duk da cece-kucen da ake yi, Babangida ya jaddada cewa tsarin dimokuradiyya ya ci gaba da wanzuwa, wanda ya sa Najeriya ta samu ci gaba a dimokuradiyya.
An kammala taron ne da kaddamar da dakin karatu na Ibrahim Badamasi Babangida na fadar shugaban kasa, inda baki da dama suka bayar da gudunmawa domin tallafawa aikin.
Daga Bello Wakili
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Babangida ya
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Burkina Faso Ya Yi Fatali Da Tayin Saudiyya Na Gina Masallatai 200 A Kasarsa
Ya soki masu ra’ayin cewa dimukradiyya wani sharadi ne na ci gaba, yana mai cewa “karya ne” shi akwai wata kasa da ta ci gaba a karkashin tsarin dimukradiyya?.
Burkina24 ta nakalto cewa “Babu wata kasa da za a iya bayyanawa da ta ci gaba a dimukradiyya.
Ya ci gaba da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da sadarwa, bayyanawa, da kuma fahimtar da mutane mene ne juyin juya hali.
Traore ya yi fice wajen yanke shawarar ce bayan hayewarsa a matsayin shugaban kasar da ke yammacin Afirka.
Shugaban mai shekaru 37 da haihuwa wanda ya hau karagar mulki a watan Satumban 2022 ta hanyar juyin mulkin da ya hambarar da shugaban kasar na wucin gadi Paul-Henri Damiba kwanan nan ya yi watsi da tayin Saudiyya na gina masallatai 200 a kasarsa.
Ya bukaci kasar Musulunci da ta gwammace ta saka hannun jari a wasu muhimman ayyukan more rayuwa wadanda za su amfani al’ummarsa kai tsaye.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp