Shirin Rigakafin Cututtuka Na UNICEF/GAVI Ya Sami Cikakken Hadin Kan Gwamnatin Jihar Jigawa
Published: 21st, February 2025 GMT
Gwamnatin jihar Jigawa ta yi alkawarin ci gaba da gudanar da ayyukan kiwon lafiya da aka gudanar karkashin hadin gwiwarta da Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF), da shirin samar da rigakafin cututtuka a kasashe masu tasowa(GAVI) a cikin shekaru uku da suka gabata.
Haɗin gwiwar wanda aka fara shi da yarjejeniyar fahimtar juna da aka rattaba hannu a shekarar 2022, an yi shi ne don haɓaka tsarin bada lafiya na jihar, da inganta tsarin rigakafi ta hanyar samar da kayan aiki da wadatattun ma’aikatan lafiya.
A wajen mika kayan aikin da aka gudanar a gidan gwamnati dake Dutse, Gwamna Umar Namadi ya ce shirin ya bayar da gudunmawa musamman wajen samar da inshorar lafiya na musamman ga mutane sama da dubu 143 a kananan hukumomi 27 na jihar.
Namadi wanda ya samu wakilcin mataimakinsa Injiniya Aminu Usman, ya ce manufofin yarjejeniyar sun yi daidai da ajandar gwamnatin jihar 12, wanda ya bai wa fannin lafiya fifiko ta hanyar sauya cibiyoyin kiwon lafiya a matakin farko tun daga tushe.
Mataimakin gwamnan wanda ya karbi tawagar UNICEF/GAVI karkashin jagorancin shugaban hukumar ta UNICEF a Najeriya, Dr Shyam Sharan-Pathak, ya ce gwamnatin za ta ci gaba da bullo da tsare-tsare don bunkasa harkar kiwon lafiya a fadin jihar.
Shi ma da yake jawabi, Kwamishinan Lafiya na Jihar, Dr Muhammed Abdullahi Kainuwa, ya ce aikin ya samu gagarumar nasara a tsawon wannan lokaci.
Ya ce an samu ingantacciyar hanyar adana alluran rigakafin, ta hanyar sayen kayayyakin adana sanyi na tafi da gidanka, da na’urorin sarrafa hasken rana kai tsaye.
Hakazalika Dakta Kainuwa ya ce, an samar da motoci 3 da suka rarraba kayayyakin aiki, sannan an dauki mutane 330 aiki.
Ya yabawa shugabannin addini da na gargajiya a jihar, bisa goyon bayan da suka bayar wajen wayar da kan jama’a a tsawon shekaru 3 da aka yi aikin.
A nasa jawabin babban sakataren ma’aikatar lafiya ta jihar Dr Kabiru Ibrahim, ya yabawa gwamna Namadi bisa jajircewarsa.
Dr Kabiru, ya lura cewa, kudurin gwamnatin na bin ka’idoji da manufofin ma’aikatar lafiya ta tarayya abin yabawa ne matuka.
Shi ma da yake nasa jawabin, babban sakataren hukumar kula da lafiya matakin farko na jihar, Dokta Shehu Sambo, ya ce yarjejeniyar ta jawo sabbin dokoki da suka shafi kiwon lafiya a jihar.
Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, shirin karfafa tsarin kula da lafiya a matakin farko shiri ne na hadin gwiwa na tsawon shekaru 3 (wato daga shekarar2022 zuwa watan Maris na 2025) tsakanin GAVI da jihohi 8 na Najeriya wanda jihar Jigawa na daga cikinsu.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa kiwon lafiya
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu Ya Kaddamar Da Ci Gaba Da Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna
Da yake jawabi a madadin shugaban kasa, Gwamna Uba Sani ya bayyana mahimmancin hanyar wadda ta hada babban birnin tarayya da jihohi sama da 12 dake fadin shiyyar Arewa ta tsakiya, Arewa maso Yamma, da Arewa maso Gabas.
A yayin taron da aka yi a Jere a karamar hukumar Kagarko a ranar Lahadin da ta gabata, Gwamna Sani ya bayyana cewa, an yi biris da aikin hanyar na tsawon shekaru da dama, wanda ya janyo asarar rayuka da kuma illa ga ci gaban tattalin arzikin yankin.
Sai dai Gwamnan ya kafa uzurin cewa, baya ga kudade, rashin tsaro da ake fama da shi a hanyar Kaduna zuwa Abuja a lokacin ne kamfanin Berger ya ki zuwa wurin domin ci gaba da aiki.
Amma a yanzu, hanyoyin da aka bi na magance matsalar tsaro yana haifar da sakamako mai kyau, domin masu ababen hawa na iya bin hanyar ba tare da fargabar an kai musu hari ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp