Gwamnatin jihar Jigawa ta yi alkawarin ci gaba da gudanar da ayyukan kiwon lafiya da aka gudanar karkashin hadin gwiwarta da Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF), da shirin samar da rigakafin cututtuka a kasashe masu tasowa(GAVI) a cikin shekaru uku da suka gabata.

Haɗin gwiwar wanda aka fara shi da yarjejeniyar fahimtar juna da aka rattaba hannu a shekarar 2022, an yi shi ne don haɓaka tsarin bada lafiya na jihar, da inganta tsarin rigakafi ta hanyar samar da kayan aiki da wadatattun ma’aikatan lafiya.

A wajen mika kayan aikin da aka gudanar a gidan gwamnati dake Dutse, Gwamna Umar Namadi ya ce shirin ya bayar da gudunmawa musamman wajen samar da inshorar lafiya na musamman ga  mutane sama da dubu 143 a kananan hukumomi 27 na jihar.

Namadi wanda ya samu wakilcin mataimakinsa Injiniya Aminu Usman, ya ce manufofin yarjejeniyar sun yi daidai da ajandar  gwamnatin jihar 12, wanda ya bai wa fannin lafiya fifiko ta hanyar sauya cibiyoyin kiwon lafiya a matakin farko tun daga tushe.

Mataimakin gwamnan wanda ya karbi tawagar UNICEF/GAVI karkashin jagorancin shugaban hukumar ta UNICEF a Najeriya, Dr Shyam Sharan-Pathak, ya ce gwamnatin za ta ci gaba da bullo da tsare-tsare don bunkasa harkar kiwon lafiya a fadin jihar.

Shi ma da yake jawabi, Kwamishinan Lafiya na Jihar, Dr Muhammed Abdullahi Kainuwa, ya ce aikin ya samu gagarumar nasara a tsawon wannan lokaci.

Ya ce an samu ingantacciyar hanyar adana alluran rigakafin, ta hanyar sayen kayayyakin adana  sanyi na tafi da gidanka,  da na’urorin sarrafa hasken rana kai tsaye.

Hakazalika Dakta Kainuwa ya ce, an samar da  motoci 3 da suka rarraba kayayyakin aiki, sannan an dauki  mutane 330 aiki.

Ya yabawa shugabannin addini da na gargajiya a jihar, bisa goyon bayan da suka bayar wajen wayar da kan jama’a a tsawon shekaru 3 da aka yi aikin.

A nasa jawabin babban sakataren ma’aikatar lafiya ta jihar Dr Kabiru Ibrahim,  ya yabawa gwamna Namadi bisa jajircewarsa.

Dr Kabiru, ya lura cewa, kudurin gwamnatin na bin ka’idoji da manufofin ma’aikatar lafiya ta tarayya abin yabawa ne matuka.

Shi ma da yake nasa jawabin, babban sakataren hukumar kula da lafiya matakin farko na jihar, Dokta Shehu Sambo, ya ce yarjejeniyar ta jawo sabbin dokoki da suka shafi kiwon lafiya a jihar.

Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, shirin karfafa tsarin kula da lafiya a matakin farko shiri ne na hadin gwiwa na tsawon shekaru 3 (wato daga shekarar2022 zuwa  watan Maris  na 2025) tsakanin GAVI da jihohi 8 na Najeriya wanda jihar  Jigawa na daga cikinsu.

 

Usman Muhammad Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa kiwon lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

Juyin-juya-halin Kyautata Muhalli: Rawar Da Kasar Sin Ke Takawa Wajen Samar Da Makoma Mai Kyau

Jarin da kasar Sin ke zubawa wajen inganta lafiyar muhalli mai dorewa a duniya ya nuna muhimmiyar rawar da take takawa ta wannan fuskar. A shekarar 2024, kasar ta jagoranci duniya wajen zuba jarin sauya makamashi, inda ta zuba dalar Amurka biliyan 818 a wannan bangare. Wannan jarin ya sanya kasar Sin ta zama cibiyar samar da makamashi mai tsafta a duniya domin ita ke da kusan kashi 50 cikin dari na tasoshin samar da man “hydrogen” mara gurbata muhalli a duk duniya.

Kasar Sin ta nuna wa duniya kyakkyawan misali abin koyi kamar yadda Shugaba Xi na kasar ke ci gaba da yayata muhimmancin kiyaye halittun doron kasa da kuma maye makamashi mai gurbata muhalli da mai tsafta. Shi ya sa ficewa daga yarjejeniyar shawo kan sauyin yanayi da Amurka ta yi kwanan nan, babban abin kunya ne a huldar da ta shafi kasashen duniya.

Alfanun kiyaye lafiyar muhalli bai tsaya kawai ga kiwon lafiyar halittu ba, ya kuma kunshi bude sabbin damammaki na ayyukan yi da bunkasa tattalin arziki. Hakika, yana da ban sha’awa, a ga manyan kasashe suna kara yin hobbasa wajen samar da kyakkyawar makoma mai dorewa ga dukkan bil’adama.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsarin Fansho Na Jihar Jigawa Ya Yi Wa Sauran Jihohi Zarra- Premium Pension
  • UNICEF Ya Jinjinawa Jihar Jigawa
  • Jihar Kano Ta Samar Da Wani Salo Na Bunkasa Ilmin Addinin Musulunci A Jihar
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar Da Shirin Da’awah Na Mata A Jihar Jigawa
  • NAJERIYA A YAU: Tanadin Dokar Kasa Kan Kirkirar Gwamnatin Bibiya A Kano
  • Matasan Jihar Jigawa Sun Karrama Gwamna Umar Namadi
  • UNICEF Ya Bukaci Hadin Kai Don Inganta Rayuwar Kananan Yara A Jigawa
  • Juyin-juya-halin Kyautata Muhalli: Rawar Da Kasar Sin Ke Takawa Wajen Samar Da Makoma Mai Kyau
  • Gwamnatin Gombe ta horar da makiyaya kan sabbin hanyoyin kiwo