UNICEF Ya Jinjinawa Jihar Jigawa
Published: 21st, February 2025 GMT
Asusun kula da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF, ya ce zai ci gaba da tallafa wa jihar Jigawa wajen gina tsarin kiwon lafiya na al’umma.
Shugaban hukumar UNICEF a Najeriya, Dr. Shyam Sharan-Pathak ya bayyana haka a wajen bikin mika aikin ga gwamnatin jihar Jigawa na tsawon shekaru 3 na GAVI, a hukumance a Dutse babban birnin jihar.
A cewarsa, UNICEF za ta ci gaba da tallafa wa jihar don bunkasa muhimman ayyuka daga cibiyoyin kula da lafiya a matakin farko na PHC, gami da ayyukan rigakafi na yau da kullun.
Dokta Shyam ya ci gaba da bayyana cewa, gagarumin ci gaban da aka samu ta hanyar shirin, shaida ce ta hadin gwiwa da jajircewa ga kowane yaro, matasa da uwa a jihar da ma fadin kasar nan.
Shugaban ma’aikatan ya yaba da gudunmawar sama da naira miliyan 879 a matsayin tallafin hadin gwiwa na shirin fahimtar juna da gwamnatin jihar Jigawa ta yi, wanda hakan ya sa gwamnatin jihar ta ware kashi 15.6% na kasafin jihar ga sashen kiwon lafiya.
Ya ce, UNICEF ta yaba da GAVI, kawancen rigakafin, saboda tallafin da suke bayarwa don haɓaka ayyukan PHC, don inganta ɗaukar rigakafin yau da kullun da kuma isar da ingantaccen shirin kula da lafiya.
A nasa jawabin, gwamna Umar Namadi ya yabawa hukumar UNICEF da abokan hulda, bisa goyon bayan da suka baiwa fannin kiwon lafiya a jihar a tsawon shekarun da suka gabata na aikin.
Namadi, ya yi nuni da cewa, gwamnatin ta fara aikin farfado da fannin lafiya a matakin farko a jihar.
USMAN MZ
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jugawa Lafiya jihar Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
Dakatar da Gwamnan Ribas zubar da ƙimar Nijeriya ne a idon duniya — Jonathan
Tsohon Shugaban Nijeriya, Goodluck Jonathan ya ce dakatar da Gwamnan Ribas, Similanayi Fubara da aka yi kwanan nan zubar da ƙimar ƙasar ne a idon duniya.
Tsohon shugaban ya ce ba daidai ba ne dakatar da Gwamnan Ribas da mataimakiyarsa, Ngozi Odu, da ’yan majalisar dokokin jihar, wanda Shugaba Bola Tinubu ya yi a makon jiya.
An ayyana zaman makoki na kwana uku bayan kashe mutum 44 a Nijar An yi wa wata karya tiyatar ceton raiChannels TV ta ruwaito Jonathan yana bayyana haka yayin da yake jawabi a matsayin shugaban taro wanda gidauniyar Haske Satumari ta shirya a ranar Asabar a Abuja.
Jonathan wanda kuma tsohon Gwamnan Jihar Bayelsa ne, ya bayyana rashin jin daɗinsa kan matakin na cire zaɓaɓɓun shugabanni da aka yi.
“Wannan matakin da aka ɗauka zai ɓata sunan Nijeriya ne a idon duniya,” in ji shi.
Jonathan ya ce duk da cewar akwai buƙatar ɗaukar matakan da za su magance rikicin siyasar da ya dabaibaye Jihar Ribas na tsawon lokaci, a cewarsa dakatar da waɗanda mutane suka zaɓa a matsayin shugabanninsu bai dace ba.
Ya ƙara da cewa ya san bai kamata a matsayinsa tsohon shugaban ƙasa ya cika maganganu barkatai a game da abubuwan da suke a ƙasar ba, amma “yadda ake kallon Nijeriya yana ta’allaƙa ne a kan matakan ɓangaren zartaswa da majalisa da na shari’a suka ɗauka,” in ji shi.
A farkon makon da muka yi bankwana, Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya kafa dokar ta ɓaci a Jihar Ribas, ya kuma dakatar da gwamna da mataimakiyarsa da dukkan ‘yan majalisar dokokin jihar na tsawon watanni shida.