Jimi’in ofishin siyasa na kungiyar jihadul-Islami ya bayyana cewa: Marigayi Sayyid Hasan Nasrallah ya baiwa Falastinu da gwagwarmaya abin da harshe ba zai iya siffanta shi ba

Mamba a ofishin siyasa na kungiyar gwagwarmaya ta Jihadul-Islami ta Falasdinu Ihsan Ataya ya yaba da irin tsayin dakan da Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta yi a fagen goyon bayan hakkokin Falasdinawa da gwagwarmayarsu, yana mai jaddada cewa: Shahidin al’ummar Sayyed Hassan Nasrallah ya gabatar wa Falasdinu da gwagwarmaya abin da harshe ba zai iya ambata ba.

A cikin wata hira ta musamman da ya yi da tashar talabijin ta Al-Alam, Adaya ya yi cikakken bayani kan yarjejeniyar musayar fursunoni tsakanin ‘yan gwagwarmayar Falasdinawa da yahudawan sahyoniya, yana mai jaddada cewa: Gwagwarmaya tana ci gaba da tafiya a kan tabbataccen matsayi domin cimma manufofinta duk kuwa da kalubalen da ake fuskanta.

Har ila yau ya tabo matsayar da ‘yan gwagwarmaya suke fuskanta na makircin kasa da kasa da ke yunkurin raba al’ummar Falastinu da tushensu na asali, yana mai jaddada cewa: Tsayin dakan ‘yan gwagwarmaya da hadin kansu sune mafi girman makamai wajen tunkarar duk wani makircin wuce gona da iri kan al’ummar Falasdinu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Palasdinawa Ne Zasu Fayyanace Makomarsu Ba Wasu Dan Mulkin Mallaka Ba: Qalibof

Shugaban majalisar dokokin kasar Iran Muhammad Bakir Qalibof ya bayyana cewa falasdinawa masu kasa ne zasu fayyace makomar kasarsu, don haka shirin da wasu manya-manyan kasashen duniya suke dashi a kan makomar Falasdinu da Falasdinawa ba dai-dai bane kuma zamu yi yaki da shi.

Tashar talabijan ta Presstv a nan Teran ta nakalto shugaban majalisar dokokin kasar Iran Mohammada Bakir Qolibft yana fadar haka a taron shuwagabannin majalisun dokoki na kasashen Asia a birnin Baku na kasar Azaibaijan.

Qolibof ya kuma kara da cewa shirin shugaban kasar Amurka yake yi na kwace gaza da kuma inda za’a maida Falasdinawa ba zai kai ga nasara ba.

Qalibof ya yi allawadai wadai da shugaba Trump kan shishigin da yake yi a cikin al-amuran Falasdinawa, da kuma yin watsi da kokarin Falasdinawa a gaza suke yi don kwato kasarsu.

Ya ce Iran ba za ta amince da duk wata kasa mai jin tana da karfi wacce za ta dorawa falasdinawa tunaninsa ba.

Shugaban majalisar ya bayyana cewa yakin da HKI ta fafata da falasdinawa a Gaza, da kuma kungiyar Hizbulla a kasar Lebanon, sun bayyana raunin HKI a fili, wannan duk tare da dukkan tallafin da take samu daga kasashen yamma musamman Amurka.

Daga karshe ya ce dole ne a sami yentacciyar kasar Palasdinu mai zaman kanta nan gaba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Limamin  Juma’a Na Tehran Ya Jaddada Muhimmancin Hadin Kai A Tsakanin Al’ummar Musulmi
  • Tashar Jiragen Sama Ta Rafikul Hariri Int. Na Birnin Beirut Yana Ciki Da Masu Shiga Kasar Saboda Jana’izar Shaheed Nasarallah
  • Jami’an Diblomasiyya Daga Kungiyar G20 Da Dama Sun Isa Afrika Ta Kudu
  • Babban Kwamandan IRGC Ya Bayyana Cewa: Amurka Da Isra’ila Ba Su Yi Nasara A Yakin Gaza Ba
  • An rufe Jami’ar Kogi saboda zanga-zangar ɗalibai
  • Palasdinawa Ne Zasu Fayyanace Makomarsu Ba Wasu Dan Mulkin Mallaka Ba: Qalibof
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa; Yahudawan Sahayoniyya Sun Kasa Murkushe Gwagwarmaya
  • ASUU Reshen Jami’ar KASU Ta Tsunduma Yajin Aikin Sai Baba-ta-gani
  • Jagora Ya Gana Da Shuwagabannin Kungiyar Jihadul Islami A Nan Tehran