Gwamnatin kasar Iran ta gargadi hukumar IAEA mai kula da al-amuran makamashin nukliya a duniya, bayan da babban sakataren kungiyar Rafaei Grossy ya fita daga matsayin dan ba ruwammu, a cikin harkokin siyasa a aikinsa, inda ya furta wasu jawabai dangane da shirin makamashin nukliya na kasar Iran.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Gorossi ya fita daga matsayinsa na gwararre da kuma masanin harkokin makamashin nukliya ya kuma dauki bangare a wani taro da yan jirudu da ya gabatar a birnin Tokyo na kasar Japan.

A cikin jawabin da yayi wa yan jaridu Grossi ya Iran tana ‘gasa makamashin Uranium har zuwa kasha 60% wanda ya kusan kaiwa ga makamashin Nukliya, sannan bata bawa hukumar IAEA hadin kai da yakamata.

Bayan wannan zancen na hukumar makamashin nukliya ta fitar da bayani inda take tuhumar Grossi da daukan bangare, kuma hukumarsa tana iya rasa iran ‘amincewar Iran’ da ayyukanta.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: makamashin nukliya

এছাড়াও পড়ুন:

Thomas Friedman: Trump Yana Son Ci Gaba Da Zama Shugaban Kasar Amurka Har Abada

Fitaccen dan jarida na Amurka wanda  Patrick Heili ya yi hira da shi ta  Podcast, ya bayyana cewa; Shugaban kasar Amurka Donald Trump yana son ya ci gaba da zama akan kujerar mulki har abada.

Hirar da Thomas Friedman ta mayar da hankali ne akan salon mulkin Donald Trump da yadda yake son sauya yadda Amurka take a cikin kwanaki 100 na farkon mulkinsa.

Thomas Friedman ya ya bayyana yadda shugaba kasar ta Amurka Donald Trump yake kokarin kwaikwayon salon mulkin shugaban kasar China Xi Jin Ping da kuma na kasar Rasha Vladmir Putin da Fira ministan Isra’ila Benjamin Netanyahu.

Shi kuwa mai gabatar da shirin  Patrick Heili ya yi ta’aliki da cewa, Trump yana kallon wadannan shugabannin a matsayin masu karfi a cikin duniyar da take cike da raunana, kuma shi Donald Trump yana son ya shimfida ikonsa a cikin duniya baki daya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Thomas Friedman: Trump Yana Son Ci Gaba Da Zama Shugaban Kasar Amurka Har Abada
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kaddamar Da Rangadi A Karamar Hukumar Jahun
  • Tashar Jiragen Sama Ta Rafikul Hariri Int. Na Birnin Beirut Yana Ciki Da Masu Shiga Kasar Saboda Jana’izar Shaheed Nasarallah
  • Trump Yana Son Ganin Bayan Shugaban Kasar Ukraine Volodimir Zelezky Daga Kujerar Shugabancin Kasarsa
  • INEC Ta Buƙaci Majalisa Ta kirkiro Dokar Hana ‘Yan Siyasa Zuwa Rumfunan Zabe Da Maƙudan Kuɗaɗe
  • An Haramta Wa Tankokin Man fetur Da Ke Jigilar Lita 60,000 Zirga-zirga A Faɗin Titunan Nijeriya 
  • An rufe Jami’ar Kogi saboda zanga-zangar ɗalibai
  • Hisbah ta rufe gidajen rawa a Katsina
  • Kasar Iran Ta Jaddada Aniyarta Ta Daukan Fansa Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila