Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kaddamar Da Rangadi A Karamar Hukumar Jahun
Published: 21st, February 2025 GMT
Kwamatin lura da kananan hukumomi na majalisar dokokin jihar Jigawa ya kaddamar da rangadi na yini biyu a karamar hukumar Jahun, domin tantance kwazon karamar hukumar ta fuskar gudanar da ayyukan raya kasa da sha’anin mulki da kashe kudade.
Shugaban kwamatin kuma wakilin mazabar Gwiwa, Alhaji Aminu Zakari, ya ce ziyarar na daga cikin ayyukan majalisa da suka hada da duba kasafin kudi da yin doka da kuma tantance abubuwan da gwamnati ta ke gudanarwa kamar yadda tsarin mulki ya tanadar.
Ya ce a lokacin wannan ziyara, kwamatin zai tantance kundin bayanan ayyukan raya kasa da rahoton zangon shekara da bayanan tarukan kwamatin tsaro da na gudanarwa.
Ya ce kwanitin zai kuma tantance bayanan ayyukan majalisar kansiloli da kuma alkaluman tattara kudaden shiga da takardun biyan kudade wato voucher daga watan October na 2024 kawo yanzu.
Alhaji Aminu Zakari ya kara da cewar, irin wannan ziyara tana bada damar ganawa gaba da gaba tsakanin bangaren majalisa da mahukuntan karamar hukuma da kuma kansiloli, dan musayen bayanai tare da bada shawarwari domin tabbatar da shugabanci nagari a matakin kananan hukumomi.
Tun farko a jawabinsa na maraba, Shugaban karamar hukumar Jahun, Alhaji Jamilu Muhammad Danmalam, ya lura cewa mu’amalarsa ta farko da ‘yan majalisa lokacin tantance kiyasin kasafin kudin 2024 ta ba shi damar samun Ilimi akan sha’anin milki, wanda hakan zai taimaka masa wajen jagorantar karamar hukumarsa cikin sauki.
Malam Jamilu Danmalam ya yi addu’a bisa fatan cewa ziyarar kwamatin za ta yi tasiri wajen inganta harkokin karamar hukumar da kuma al’ummar Jahun baki daya.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa Majalisar Dokoki karamar hukumar
এছাড়াও পড়ুন:
Jihar Kano Ta Samar Da Wani Salo Na Bunkasa Ilmin Addinin Musulunci A Jihar
Gwamnatin jihar Kano ta dauki wani gagarumin mataki na bunkasa ilimin addinin musulunci a jihar ta hanyar hada hannu da kungiyar Agaji ta Musulunci da ke Birtaniya, wato Muslim Charity For United Kingdom a turance.
Wannan haɗin gwiwar na nufin tallafa wa makarantun Islamiyya da kayayyakin koyon ilimi na zamani, da sauransu.
A cewar daraktan wayar da kan jama’a na ma’aikatar ilimi ta jihar Kano, Balarabe Abdullahi Kiru, wannan shiri ya yi daidai da kokarin da gwamnati ke yi na karfafa fannin ilimi.
Haɗin gwiwar zai magance matsalolin da ke addabar ilimin addinin Islama, da tabbatar da cewa makarantun Islamiyya sun sami tallafin da ya dace don samu ingantaccen yanayin karatu da koyarwa.
Ya yi nuni da cewa, Kwamishinan Ilimi na Jihar, Dakta Ali Haruna Makoda, ya bayyana fatan cewa, wannan hadin gwiwa zai inganta ilimin addinin Musulunci, musamman a tsarin makarantun Islamiyya.
Ya ce, shirin zai mayar da hankali ne wajen samar da kayayyakin koyo na zamani domin inganta kwazon dalibai.
Da take jawabi a madadin tawagar, shugabar kungiyar agaji ta addininMusuluncida ke Birtaniya, Dr. Samira Abubakar Abdullahi, ta bayyana cewa kungiyar na aiki tukuru a Najeriya domin tallafawa harkokin ilimi da kiwon lafiya.
Ta bayyana cewa gudummawar da suke bayarwa sun hada da shirye-shiryen gyara makarantu, ayyukan ci gaban ilimi, da ayyukan kiwon lafiya.
“Mun zo ma’aikatar don tattaunawa kan bangarorin haɗin gwiwa da kuma yi wa kwamishina bayani game da ayyukanmu,” inji ta.
Kungiyar agajin tana aiki tukuru a Najeriya don tallafawa ayyukan ilimi da kiwon lafiya.
Daga Khadija Aliyu