Babban mai kai wa Bello Turji makamai ya shiga hannu
Published: 21st, February 2025 GMT
Jami’an Tsaro a Jihar Sakkwato, sun kama babban mai yi wa Bello Turji safarar makamai, mai suna Hamza Suruddubu.
Rahotanni sun bayyana cewar ana zarginsa da yi wa wasu maharan safarar makamai a jihar.
An tara Naira 16 a taron ƙaddamar da littafin IBB Ba ni da hannu a kisan Dele Giwa — Janar BabangidaWata majiya, ta shaida wa Zagazola Makama cewa Suruddubu ɗan yankin Gabashin Sakkwato ne, kuma ya daɗe yana safarar makamai daga jihar Zamfara zuwa sansanonin ‘yan ta’adda a Gabashin Sakkwato.
“Shi ne babban mai yi wa ƙasurguman ’yan bindiga irin su Bello Turji, Boka, da Halilu Buzu safarar makamai,” in ji majiyar.
Bincike, ya nuna cewa ba makamai kawai Suruddubu ke safara ba, har da wasu kayayyakin buƙata kamar abinci da babura domin taimaka wa ’yan ta’adda a yankin.
“Har ila yau akwai rahotannin da ke nuna cewa wasu jami’an tsaro a ƙananan hukumomin Shinkafi da Isa na da hannu a safarar waɗannan makamai,” in ji majiyar.
Shugabannin al’umma da masana tsaro sun yi kira ga hukumomin tsaro da su gudanar da cikakken bincike a kan Suruddubu.
Sun buƙaci a yi binciken don gano yadda ake safarar makamai tsakanin Isa da Sabon Birni.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Safarar Makamai Zamfara zargi safarar makamai
এছাড়াও পড়ুন:
Bam ya kashe mutum 4 da jikkata wasu a Borno
Aƙalla fasinjoji huɗu ne suka mutu yayin da wasu huɗu suka jikkata sakamakon fashewar wani bam a ƙarƙashin wata motar kasuwanci a ƙaramar hukumar Biu ta Jihar Borno.
Rundunar ’yan sandan Jihar Borno ta tabbatar ta afkuwar lamarin.
Gobara ta kashe ɗan shekara 7 a sansanin ’yan gudun hijira ’Yan bindiga sun yi garkuwa da jami’in FRSC a BenuweMajiyoyin leƙen asiri sun shaidawa Zagazola Makama cewa, lamarin ya faru ne a ranar 19 ga Maris, 2025, da misalin ƙarfe 2:30 na rana a lokacin da wata mota ƙirar Golf 3 ta Wakil Fari ta tashi daga garin Kimba zuwa garin Biu.
Bayan sun isa mahaɗar Sabon Garin Kimba, motar ta taka wata nakiya (IED), wanda ya kai ga fashewa da ta kashe fasinjoji mata uku da fasinja namiji guda nan take.
Majiyar na cewar wasu fasinjoji hudu kuma sun sami raunuka daban-dabam kuma nan da nan an kai su babban asibitin Biu don yi musu jinya.
Daga bisani likitoci sun tabbatar da mutuwar wadancan mutane huɗu sannan aka ajiye su a ɗakin ajiyar gawa na asibitin kafin a miƙa su ga ’yan uwansu don yi musu jana’iza.
Bincike na farko ya nuna cewa ’yan ta’addar ISWAP ne suka dasa waɗannan bama-bamai (IEDs) a tunanin sojoji za su taka.
Jami’an soji sun tabbatar da faruwar hakan, tare da duba ƙarin barazanar da ake fuskanta daga wadannan ‘yan ta’addan don tabbatar da tsaro ga masu amfani da hanya.
Hukumomi sun kuma ƙaddamar da gangamin wayar da kan al’umma kan haɗarin bama-bamai da ba su fashe ba, don kaucewa faruwar lamari irin ya hakan.