An ƙwace miliyoyin daloli, gidajen da ke da alaƙa da Emefiele
Published: 21st, February 2025 GMT
Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Legas ta bayar da umarnin a ƙwace Dala miliyan 4.7 da Naira miliyan 830 da wasu kadarori da dama da ke da alaƙa da tsohon Gwamnan babban bankin Najeriya (CBN) Godwin Emefiele.
Da yake yanke hukunci a ranar Juma’a, Mai shari’a Yellim Bogoro, wanda a baya ya yi watsi da buƙatar kama Emefiele, ya amince da buƙatar hukumar yaƙi da yi wa tattalin arzikin ƙasa zagon ƙasa ta EFCC, wadda lauya Bilkisu Buhari-Bala ta wakilta.
Kuɗaɗen da a halin yanzu gwamnatin tarayya ta ƙwace, sun kasance a cikin asusun bankunan: First Bank, Titan Bank da Zenith Bank da wasu mutane da hukumomi suke kula da su da suka haɗa da: Omoile Anita Joy, kamfanin Deep Blue Energy Serɓice Limited, kamfanin Exactquote Bureau De Change Ltd, Kamfanin Lipam Investment Services Limited, kamfanin Tatler Services Limited, kamfanin Rosajul Global Resources Ltd, da kamfanin TIL Communication Nigeria Ltd.
Kaddarorin da aka ƙwace na wucin gadi sun haɗa da: Ɗakuna 94 na wani bene mai hawa 11 da ake ginawa a 2 Otunba Elegushi 2nd Aɓenue, Ikoyi, Legas; da AM Plaza, ofisoshi mai hawa 11 a ginin Otunba Adedoyin Crescent, Lekki Peninsula Scheme 1, a Legas; da Imore Industrial Park 1 a Esa Street, Imoore Land, a Ƙaramar Hukumar Amuwo Odofin a Legas; Mitrewood and Tatler Warehouse kusa da Elemoro, Village Owolomi, Ibeju-Lekki LGA, Lagos; da kadarori biyu da aka saya daga kamfanin Chevron Nigeria, da ke cikin rukunin gidaje na Estate Lakes a Lekki da ke Legas.
Mai shari’a Bogoro ya bayyana cewa, duk waɗannan kadarori da kuɗaɗe ne na wasu ayyuka da suka saɓawa ƙa’ida, waɗanda gwamnatin tarayyar Najeriya za ta iya kwace su.
Alƙalin ya ce: “Na ga cewa ayyukan waɗanda ake ƙara a nan ba halastattu be ne. Me zai sa su samu matsalar dala nan take, Godwin Emefiele ya bar CBN a matsayin gwamnan Banki kuma an kasa biyan albashi?
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Hana Biza: Najeriya ta cancanci a girmama ta – Babban Hafsan Tsaro
Babban Hafsan Tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa, ya gargaɗi ƙasashe cewa Najeriya ba za ta yarda da rashin girmamawa daga kowace ƙasa ba.
Ya bayyana hakan ne bayan da Ƙasar Kanada ta hana wasu jami’an sojin Najeriya takardae izinin shiga ƙasar, duk da cewa an gayyace su don halartar wasannin Invictus a Vancouver.
’Yan bindiga sun Kashe mutum 2 kan jinkirin biyan kuɗin fansa Gwamnatin Gombe ta horar da makiyaya kan sabbin hanyoyin kiwoDa yake jawabi a Hedikwatar Tsaro da ke Abuja, bayan tarbar sojojin da suka halarci gasar, Musa ya nuna takaicinsa kan yadda ake nuna wa ‘yan Najeriya rashin adalci a wasu ƙasashe.
“Mun bi dukkanin matakan da suka dace. An aiko mana da gayyata, jami’an gwamnati sun sani, kuma mun cika dukkanin sharuɗa.
“Amma, ba san dalilin da ya sa aka hana jagororin tawagarmu kamar kaftin, likitan tawaga da mai duba biza. A. Tambayar ita ce, me ya sa?” in ji shi.
Musa ya jinjina wa sojojin da suka wakilci Najeriya a gasar, inda ya tabbatar musu da cewa gwamnati ba za ta bari su wulaƙanta ba.
“Sojojinmu da suka rasa wasu sassa jikinsu ko suka samu raunuka ba za a bari a wulakanta su ba.
“Za mu ci gaba da tallafa musu domin sadaukarwarsu ba za ta tafi a banza ba,” in ji shi.
Ya jaddada cewa Najeriya ta cancanci girmamawa, kuma ba za ta yarda da rashin adalci daga kowace ƙasa ba.