Aminiya:
2025-04-16@00:32:49 GMT

An ƙwace miliyoyin daloli, gidajen da ke da alaƙa da Emefiele

Published: 21st, February 2025 GMT

Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Legas ta bayar da umarnin a ƙwace Dala miliyan 4.7 da Naira miliyan 830 da wasu kadarori da dama da ke da alaƙa da tsohon Gwamnan babban bankin Najeriya (CBN) Godwin Emefiele.

Da yake yanke hukunci a ranar Juma’a, Mai shari’a Yellim Bogoro, wanda a baya ya yi watsi da buƙatar kama Emefiele, ya amince da buƙatar hukumar yaƙi da yi wa tattalin arzikin ƙasa zagon ƙasa ta EFCC, wadda lauya Bilkisu Buhari-Bala ta wakilta.

’Yan sanda sun daƙile satar mutane, sun kama wasu 3 a Borno Ba ni da hannu a kisan Dele Giwa — Janar Babangida

Kuɗaɗen da a halin yanzu gwamnatin tarayya ta ƙwace, sun kasance a cikin asusun bankunan: First Bank, Titan Bank da Zenith Bank da wasu mutane da hukumomi suke kula da su da suka haɗa da: Omoile Anita Joy, kamfanin Deep Blue Energy Serɓice Limited, kamfanin Exactquote Bureau De Change Ltd, Kamfanin Lipam Investment Services Limited, kamfanin Tatler Services Limited, kamfanin Rosajul Global Resources Ltd, da kamfanin TIL Communication Nigeria Ltd.

Kaddarorin da aka ƙwace na wucin gadi sun haɗa da:  Ɗakuna 94 na wani bene mai hawa 11 da ake ginawa a 2 Otunba Elegushi 2nd Aɓenue, Ikoyi, Legas; da AM Plaza, ofisoshi mai hawa 11 a ginin Otunba Adedoyin Crescent, Lekki Peninsula Scheme 1, a Legas; da Imore Industrial Park 1 a Esa Street, Imoore Land, a Ƙaramar Hukumar Amuwo Odofin a Legas; Mitrewood and Tatler Warehouse kusa da Elemoro, Village Owolomi, Ibeju-Lekki LGA, Lagos; da kadarori biyu da aka saya daga kamfanin Chevron Nigeria, da ke cikin rukunin gidaje na Estate Lakes a Lekki da ke Legas.

Mai shari’a Bogoro ya bayyana cewa, duk waɗannan kadarori da kuɗaɗe ne na wasu ayyuka da suka saɓawa ƙa’ida, waɗanda gwamnatin tarayyar Najeriya za ta iya kwace  su.

Alƙalin ya ce: “Na ga cewa ayyukan waɗanda ake ƙara a nan ba halastattu be ne. Me zai sa su samu matsalar dala nan take, Godwin Emefiele ya bar CBN a matsayin gwamnan Banki kuma an kasa biyan albashi?

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun kashe mutane 40 a sabon hari a Filato

’Yan bindiga sun kashe mutane arba’in a wani hari suka kai a ƙauyen Zike, a yankin Kwall da ke Ƙaramar Hukumar Bassa a Jihar Filato.

Wani shugaban al’ummar Kwall, Wakili Tongwe, ya ce maharan sun shiga ƙauyen ne da sanyin safiyar ranar Litinin suna harbi kan mai uwa da wabi, lamarin da ya sa mazauna gujegujen neman tsira.

Ya shaida wa wa kafar talabijin ta Channels cewa wata tawagar ’yan banga, da shi kansa da wasu jami’an tsaro, suna sintiri a wani ƙauye ne lokacin da maharan suka kai harin.

Ko da yake jami’an tsaron sun yi artabu da maharan kuma sun yi nasarar fatattakar su, amma an riga an riga an kashe mutane talatin da shida nan take, wasu huɗu kuma suka mutu daga baya.

Boko Haram ta kashe mutum 300 ta kwace ƙananan hukumomi 3 a Borno — Ndume NAJERIYA A YAU: Dalilan Farfaɗowar Boko Haram A Jihar Borno

Wasu mazauna garin kuma sun samu raunukan harbin bindiga kuma suna samun kulawa a asibiti.

Hukumomin tsaro a jihar ba su yi wani sharhi ba game da harin, wanda ya zo ƙasa da makonni biyu bayan an kashe mutane hamsin da biyu a wasu ƙauyukan Karamar Hukumar Bokkos ta Jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Isra’ila ta kashe Palasdinawa 17 ta jikkata 69 a awa 24 a Gaza
  • An Kashe Sojojin Yahudawa A Gaza A Yayinda Wasu Da Dam Suka Ji Rauni
  • Sojoji sun ceto mafiya 16 da aka yi garkuwa da wasu a Filato
  • Kotu ta tsare ’yan TikTok 2 a Kano
  • Gaza: Mutane 38 Sun Yi Shahada A Yau Litinin
  • ‘Yansanda Sun Kama Wasu Da Ake Zargin Ɓarayin Wayar Wutar Lantarki Ne A Yobe
  • ’Yan bindiga sun kashe mutane 40 a sabon hari a Filato
  • Abincin karnuka ya fi namu —Fursunonin Najeriya
  • Hatsarin Mota Ya Hallaka Mutum Ɗaya A Bauchi, Wasu Sun Jikkata
  • Ta kai ƙarar kamfanin jirgi da fasinja kan kukan yaro