Aminiya:
2025-02-22@15:45:39 GMT

Karyewar Farashi: Ba mu shigo da kayan abinci daga waje ba — Minista

Published: 21st, February 2025 GMT

Gwamnatin Tarayya, ta bayyana cewa ba ta shigo da kayan abinci daga ƙasashen waje ba, duk da cewa farashin kayan abinci ya ragu a kasuwanni.

Ministan Aikin Gona da Samar da Abinci, Farfesa Abubakar Kyari, ya bayyana cewa, ko da yake gwamnatin ta yi tunanin shigo da abinci a lokacin da farashinsa ya yi tashin gwauron zabo, daga bisani ta janye wannan shawarar.

An ƙwace miliyoyin daloli, gidajen da ke da alaƙa da Emefiele Babban mai kai wa Bello Turji makamai ya shiga hannu

Ministan ya danganta saukar farashin kayan abinci da ƙoƙarin manoma da suka koma gonaki a daminar bara, wanda ya sa amfanin gona ya yi yawa.

Ya kuma buƙaci ‘yan kasuwa da su rage farashi domin jama’a su samu sauƙin rayuwa.

Sai dai wasu rahotanni sun bayyana cewa saukar farashin kayan abincin na da alaƙa da wasu dalilai da suka haɗa da shigo da wasu nau’ikan kayan abinci daga waje ba tare da haraji ba.

Wannan mataki da gwamnati ta ɗauka ya taimaka wajen ƙara wadatuwar kayan abinci a kasuwanni, lamarin da ke hana farashinsu tashi.

Har ila yau, ana cikin lokacin girbi, wanda ya sa manoma da yawa suka fito da amfanin gonarsu zuwa kasuwanni.

Yawaitar kayan abinci a hannun ’yan kasuwa ya rage farashin kayayyaki kamar shinkafa, gero, dawa, da wake.

Wani babban dalili da masana tattalin arziƙi suka bayyana shi ne, farfaɗowar darajar Naira a kasuwar musayar kuɗi.

Saukar darajar dala ya sa kayan abinci da ake shigo da su daga waje sun yi sauƙi idan aka kwatanta da watannin baya.

Tsare-tsaren da Gwamnatin Tarayya ta ɗauka domin rage tsadar rayuwa, ciki har da sauƙaƙa shigo da abinci, sun taka muhimmiyar rawa wajen rage hauhawar farashi a kasuwanni.

Wannan mataki na ci gaba da samar da sauƙi ga jama’a yayin da ake fatan farashin kayan abinci zai ci gaba da yin ƙasa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan kasuwa Kayan abinci Masara Ministan Harkokin Noma farashin kayan abinci kayan abinci da a kasuwanni

এছাড়াও পড়ুন:

Jami’an tsaron al’umma 6 sun mutu a artabu da ’yan bindiga a Sakkwato

Mutum shida daga cikin Jami’an Tsaron Al’umma na Jihar Sakkwato sun kwanta dama bayan wata musayar wuta da ’yan bindiga a Kamarar Hukumar Sabon Birni.

Wasu majiyoyi sun bayyana cewa jami’an tsaron sun gamu da ajalinsu ne a lokacin da suka kai ɗauki ga al’umma da ’yan bindiga suka kai wa hari. A hanyarsu ne ’yan bindiga suka yi musu kwanton ɓauna.

Wata majiya ta bayyana cewa abokin aikinsu ne ya kira ya sanar da cewa, ’yan bindiga suna hanyarsu ta kawo hari ƙauyensi da ke kusa da Unguwan Lalle.

“Jami’an tsaron sun nemi abin hawa daga hukumar karamar hukumar amma an hana su, saboda an hana su gudanar da ayyukan tsaro na yau da kullum su kaɗai ba tare da jami’an tsaron gwamnatin ba,” in ji majiyarmu.

NAJERIYA A YAU: Tanadin Dokar Kasa Kan Kirkirar Gwamnatin Bibiya A Kano Real Madrid ta fitar da Man City a Gasar Zakarun Turai

Da ba su samu abin hawa ba, sai suka hau baburansu suka tafi ƙauyen, amma aka yi rashin sa’a, ’yan bindigar suka yi musu kwanton ɓauna.

“Sna musayar wuta da ’yan ta’adda kafin a kashe mutum shida daga cikinsu, waɗanda daga bisani aka kawo gawarwakinsu an yi musu jana’iza,” in ji majiyar.

Lokacin da aka tuntube shi, kwamandan Rundunar Tsaro ta Jihar Sakkwato, Kanar Na-Allah Idris, ya ƙi cewa komai kan harin.

Haka nan, shugaban majalisa, Alhaji Ayuba Hashimu da memba mai wakiltar Sabon Aminu Boza sun kasa amsa kiran wayar wakilinmu.

Memba, wakiltar Sabon Birni gabas, ya tabbatar da lamarin amma ya ƙi yin ƙarin bayani saboda yankin ba a ƙarƙashinsa yake ba.

An tuntuɓi kakakin ’yan sanda na Jihar Sakkwato, ASP Ahmad Rafa’i, inda ya ce ba shi da rahoto kan lamarin.

Mai ba da shawara na musamman ga gwamna Ahmed Aliyu Ahmed kan sha’anin tsaro, Ahmed Usman ya tabbatar da harin, kuma ana ci gaba da bincike domin gano gaskiyar abin da ya faru.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Alhassan (a) 20
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Alhassan (a) 19
  • Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kano ta raba kayan tallafi
  • ‘Yan Fansho Na FRCN Da NTA Sun Yabawa Gwamnati Bisa Amincewa Da Biyan Harkokinsu
  • Trump Yana Son Ganin Bayan Shugaban Kasar Ukraine Volodimir Zelezky Daga Kujerar Shugabancin Kasarsa
  • Kayan Abinci: Gwamnatin Nijeriya Ta Buƙaci ‘Yan Kasuwa Su Rage Farashi
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Ba Za Mu Sauke Farashin Burodi Ba —’Yan kasuwa
  • Jami’an tsaron al’umma 6 sun mutu a artabu da ’yan bindiga a Sakkwato
  • Gobara ta ƙone gidaje, dabobbi da kayan abinci a Kano