Karyewar Farashi: Ba mu shigo da kayan abinci daga waje ba — Minista
Published: 21st, February 2025 GMT
Gwamnatin Tarayya, ta bayyana cewa ba ta shigo da kayan abinci daga ƙasashen waje ba, duk da cewa farashin kayan abinci ya ragu a kasuwanni.
Ministan Aikin Gona da Samar da Abinci, Farfesa Abubakar Kyari, ya bayyana cewa, ko da yake gwamnatin ta yi tunanin shigo da abinci a lokacin da farashinsa ya yi tashin gwauron zabo, daga bisani ta janye wannan shawarar.
Ministan ya danganta saukar farashin kayan abinci da ƙoƙarin manoma da suka koma gonaki a daminar bara, wanda ya sa amfanin gona ya yi yawa.
Ya kuma buƙaci ‘yan kasuwa da su rage farashi domin jama’a su samu sauƙin rayuwa.
Sai dai wasu rahotanni sun bayyana cewa saukar farashin kayan abincin na da alaƙa da wasu dalilai da suka haɗa da shigo da wasu nau’ikan kayan abinci daga waje ba tare da haraji ba.
Wannan mataki da gwamnati ta ɗauka ya taimaka wajen ƙara wadatuwar kayan abinci a kasuwanni, lamarin da ke hana farashinsu tashi.
Har ila yau, ana cikin lokacin girbi, wanda ya sa manoma da yawa suka fito da amfanin gonarsu zuwa kasuwanni.
Yawaitar kayan abinci a hannun ’yan kasuwa ya rage farashin kayayyaki kamar shinkafa, gero, dawa, da wake.
Wani babban dalili da masana tattalin arziƙi suka bayyana shi ne, farfaɗowar darajar Naira a kasuwar musayar kuɗi.
Saukar darajar dala ya sa kayan abinci da ake shigo da su daga waje sun yi sauƙi idan aka kwatanta da watannin baya.
Tsare-tsaren da Gwamnatin Tarayya ta ɗauka domin rage tsadar rayuwa, ciki har da sauƙaƙa shigo da abinci, sun taka muhimmiyar rawa wajen rage hauhawar farashi a kasuwanni.
Wannan mataki na ci gaba da samar da sauƙi ga jama’a yayin da ake fatan farashin kayan abinci zai ci gaba da yin ƙasa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: yan kasuwa Kayan abinci Masara Ministan Harkokin Noma farashin kayan abinci kayan abinci da a kasuwanni
এছাড়াও পড়ুন:
Ban bai wa majalisa haƙuri ba — Natasha
Sanata mai wakilatar Kogi ta Tsakiya, Natasha Akpoti-Uduaghan, ta musanta batun da ake yaɗawa cewa ta bai wa Majalisar Dattawa haƙuri.
A wata sanarwa da ta fitar ranar Litinin, Natasha ta ce tana na kan batunta, kuma ba za ta taɓa bai wa majalisar haƙuri a kan gaskiyarta ba.
Fursunoni 12 sun tsere bayan fasa gidan yari a Kogi Za mu farfaɗo da Madatsar Ruwa ta Biu — ZulumIdan za a tuna dai majalisar ta dakatar da Natasha tsawon watanni shida tare da dakatar da albashi da alawus-alawus ɗinta ne bisa saɓa wa dokokin majalisar da kwamitin ƙorafi da ladabtarwa ya tabbatar.
Lamarin dai na zuwa ne a daidai lokacin da kuma Sanata Natasha take ci gaba da zargin shugaban majalisar, Godswil Akpabio, da cin zarafinta.
Daga bisani kuma Natasha ta shigar da koken nata a Majalisar Ɗinkin Duniya.
“Zan ci gaba da yaƙi domin ƙwato ‘yancin matan Najeriya har sai ranar da aka fara sauraronmu. Yunƙurin da ake yi domin rufe bakina ba na wasa ba ne, amma ko a jikina.
“Gaskiyar wasan kwaikwayon da ake yi akan idon ‘yan Najeriya za ta bayyana watarana, sannan duk ‘yan rashawar da suka mamaye gwamnatin za su yi bayani dalla-dalla,” in ji Natasha.
“Don haka ina kira gare ku, da ku yi watsi da da duk wani rahoto da kuka ci karo da shi cewa na bai wa majalisa haƙuri, domin ba gaskiya ba ne.
“Ina na kan batuna, kuma zan ci gaba da yaƙi a kan gaskiyata duk rintsi duk wuya.
To sai dai Natasha na wannan maganar ne a daidai lokacin da hukumar zaɓe ta kasa ke bayyana cewa ta samu takardar neman yi wa ‘yar majalisar kiranye daga mazabarta.
Sakatariyar hukumar Rose Oriarana-Anthony ce ta bayyana hakan inda ta ce takardar ta iske ta ne a ranar Litinin.