Hukumar bayar da gudunmawar fansho ta Jihar Jigawa da Kananan Hukumomin jihar ta kulla yarjejeniyoyi da wasu mashahuran Hukumomin Asusun Fansho guda shida (PFA) da nufin tabbatar da tafiyar da kudaden fansho na jihar yadda ya kamata.

Shugaban ma’aikata na jiha Alhaji Muhammad K Dagaceri wanda ya jagoranci rattaba hannu kan yarjejeniyar a madadin gwamnatin jihar Jigawa a gidan fensho na Dutse ya ce taron yana kara jaddada kudirin gwamnati na  tabbatar da gaskiya da inganci a tsarin tafiyar da fansho.

Ya kuma jaddada mahimmancin kula da harkokin kudi da kuma bukatar samar wa wadanda suka yi ritaya kudaden fansho domin ci gaba da gudanar da rayuwarsu.

“Wannan yarjejeniya ta nuna wani gagarumin ci gaba a kokarin da muke yi na ganin cewa ma’aikatanmu da suka yi ritaya sun samu haƙƙinsu a kan lokaci.”

Alhaji Muhammad Dagaceri ya ci gaba da bayyana cewa, an zabo shugabannin asusun fansho ne ta hanyar tantancewa.

A cewarsa, masu gudanar da ayyukan za su samar da ingantattun ayyukan gudanarwa, da suka hada da dabarun saka hannun jari, da kula da ayyukan asusu da inganta ayyukan abokan ciniki.

Shugaban Ma’aikatan ya ce Hukumar Fansho ta Jihar Jigawa za ta sa ido a kan hadakar, tare da tabbatar da cewa PFA sun bi ka’ida da kuma cika alkawuran da suka dauka ga Jihar da masu karbar fansho.

Ya jaddada sadaukarwar gwamnatin Gwamna Umar Namadi wajen kyautata jin dadin ma’aikatan da suka yi ritaya, yana mai cewa wannan wani bangare ne na kokarin inganta ayyukan gwamnati da kuma kaucewa rikon sakainar kashi a harkokin tafiyar da dukiyar jihar.

Da yake jawabi a madadin  hukumomin na PFA Manajan Daraktan Asusun Fansho na Premium Hamisu Bala Idris, ya tabbatar wa hukumar cewa PFA  da aka zaba za su ci gaba da aiki yadda ya kamata ta hanyar bin duk wasu sharuddan da ke cikin yarjejeniyar.

Hamisu, ya bayyana tsarin fansho na jihar Jigawa a matsayin wanda ya fi kowanne a fadin kasar nan.

A nasa jawabin, Shugaban  Hukumar  Fansho ta Jihar Jigawa da Kananan Hukumomi, Dokta Bilyaminu Shitu Aminu ya bayyana cewa, zababbun  asusun fansho guda shida da za su kula da dukiyar hukumar su ne, Premium Pension Fund (Lead PFA), da PAL Pension, da GT Pension, da  NLPC Pension, da  Norrenberger Pension da Cruder.

Dakta Bilyaminu Shitu Aminu ya yabawa Gwamna Malam Umar  Namadi bisa gagarumin goyon bayan da ya bayar ga shirin da ya sa Jihar ta zama abin koyi a kasar nan.

Usman Muhammad Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa Yarjejeniya Jihar Jigawa jihar Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Dakatar da Gwamnan Ribas zubar da ƙimar Nijeriya ne a idon duniya — Jonathan

Tsohon Shugaban Nijeriya, Goodluck Jonathan ya ce dakatar da Gwamnan Ribas, Similanayi Fubara da aka yi kwanan nan zubar da ƙimar ƙasar ne a idon duniya.

Tsohon shugaban ya ce ba daidai ba ne dakatar da Gwamnan Ribas da mataimakiyarsa, Ngozi Odu, da ’yan majalisar dokokin jihar, wanda Shugaba Bola Tinubu ya yi a makon jiya.

An ayyana zaman makoki na kwana uku bayan kashe mutum 44 a Nijar An yi wa wata karya tiyatar ceton rai

Channels TV ta ruwaito Jonathan yana bayyana haka yayin da yake jawabi a matsayin shugaban taro wanda gidauniyar Haske Satumari ta shirya a ranar Asabar a Abuja.

Jonathan wanda kuma tsohon Gwamnan Jihar Bayelsa ne, ya bayyana rashin jin daɗinsa kan matakin na cire zaɓaɓɓun shugabanni da aka yi.

“Wannan matakin da aka ɗauka zai ɓata sunan Nijeriya ne a idon duniya,” in ji shi.

Jonathan ya ce duk da cewar akwai buƙatar ɗaukar matakan da za su magance rikicin siyasar da ya dabaibaye Jihar Ribas na tsawon lokaci, a cewarsa dakatar da waɗanda mutane suka zaɓa a matsayin shugabanninsu bai dace ba.

Ya ƙara da cewa ya san bai kamata a matsayinsa tsohon shugaban ƙasa ya cika maganganu barkatai a game da abubuwan da suke a ƙasar ba, amma “yadda ake kallon Nijeriya yana ta’allaƙa ne a kan matakan ɓangaren zartaswa da majalisa da na shari’a suka ɗauka,” in ji shi.

A farkon makon da muka yi bankwana, Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya kafa dokar ta ɓaci a Jihar Ribas, ya kuma dakatar da gwamna da mataimakiyarsa da dukkan ‘yan majalisar dokokin jihar na tsawon watanni shida.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kantoman Ribas ya naɗa sabon Sakataren Gwamnati
  • NUJ Ta Bada Tallafin Azumi Ga Iyalan Mambobinta Da Suka Rasu A Jihar Kebbi
  • Fursunoni 12 Sun Tsere Daga Gidan Yari A Jihar Kogi
  • Gwamna Uba Sani Ya Nada Sarkin Kauru Amirul Hajj Na Shekarar 2025
  • Dokar Ta-ɓaci A Ribas: Gwamnonin PDP Sun Ƙalubalanci Hukuncin Tinubu A Kotun Ƙoli
  • Wasu manyan ’yan Nijeriya sun yi wa Gwamna Radda ta’aziyya a Saudiyya
  • Gobara ta tashi a gidan mai sakamakon fashewar tanka a Neja
  • Gwamnatin Jigawa Ta Nanata Dokar Haramta Kiwon Dare
  • Hikimar Gwamnatin Jihar Jigawa Na Kaddamar Da Shirin Gina Rijiyoyin Burtsatsan Noman Rani
  • Dakatar da Gwamnan Ribas zubar da ƙimar Nijeriya ne a idon duniya — Jonathan