A yau Jumma’a ne jirgin saman da kasar Sin ta kera samfurin AS700D mai amfani da makamashin lantarki ya kammala tashinsa na farko cikin nasara, wanda ya nuna sabon ci gaban da kasar ta samu a sashen samar da kayayyakin sufurin jiragen sama masu amfani da makamashi mai tsafta a fannin tattalin arzikin jirage masu tashi kasa-kasa daga doron kasa, kamar yadda kamfanin sarrafa jiragen sama na kasar Sin (AVIC) wanda ya kera jirgin ya sanar.

Kamfanin AVIC ya bayyana cewa, wannan muhimmin ci gaba ya tabbatar da girman iya kere-kere da ka’idoji na kasar Sin bisa kera jirgin na AS700D da kanta ba tare da sa hannun kowa ba, tare da samar da tanadin da ake bukata na fasaha don bunkasa kera jirage masu amfani da makamashin lantarki da za su biyo baya.

Jirgin na AS700D ya gudanar da tashin na farko ne da safiyar yau Juma’a a Jingmen na lardin Hubei da ke tsakiyar kasar Sin.

Bayanai sun nuna jirgin ya tashi sannu a hankali a tsaye sannan ya yi sauri ya nausa zuwa tsayin mita 50. Bayan ya yi shawagi a takaice, sai ya sauka a tsaye kana daga bisani ya tsaya sannu a hankali. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Sin Ta Bukaci G20 Ta Zama Karfin Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali A Duniya

Bugu da kari, ministan ya ce bana lokaci ne na Afrika, duba da cewa za a gudanar da taron kolin G20 a nahiyar Afrika a karo na farko tun bayan da AU ta zama cikakkiyar mamba.

Ya ce ya kamata a saurari kiraye-kirayen nahiyar, a kuma yi la’akari da damuwarta, kana a taimakawa ayyukanta da samar da damar wanzar da zaman lafiya da ci gaba a nahiyar.

Ministan ya kuma tabbatar da cewa, kasar Sin na goyon bayan jama’ar nahiyar su warware matsalolin da kansu, kuma tana adawa da kasashen waje su rika tsoma baki cikin harkokin kasashen Afrika. (Fa’iza Mustapha)

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kungiyar Hizbullah Ta Lebanon Ta Jaddada Rashin Amincewarta Da Mika Kan Kasar Ga Amurka Da Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Wasu sassan Abuja za su kasance cikin duhu a ƙarshen mako – TCN
  • Kasar Sin Ta Bukaci G20 Ta Zama Karfin Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali A Duniya
  • Amurka Ta Bawa HKI Makami Mai Karfi, MK-87
  • Yadda Za A Kare Yara Daga Barazanar Intanet
  • Babban Kwamandan IRGC Ya Bayyana Cewa: Amurka Da Isra’ila Ba Su Yi Nasara A Yakin Gaza Ba
  • EFCC ta gargaɗi ciyamomi kan amfani da kuɗaɗen jama’a a Gombe
  • Gwamnati Za Ta Haramta Amfani Da Tankoki Masu Ɗaukar Lita 60,000 Aiki Daga Maris 1
  • UNICEF Ya Bukaci Hadin Kai Don Inganta Rayuwar Kananan Yara A Jigawa