Aminiya:
2025-02-22@15:46:38 GMT

Zaɓen ƙananan hukumomin Osun na nan daram – Gwamna Adeleke

Published: 21st, February 2025 GMT

Gwamnan Jihar Osun, Ademola Adeleke ya ce ya sha alwashin cewa zaɓen ƙananan hukumomin da za a yi a jihar a gobe Asabar zai gudana kamar yadda aka tsara.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a matsayin martani kan shawarar da ministan shari’a na Najeriya, Lateef Fagbemi, wanda ya buƙaci gwamnatin jihar ta dakatar da yunƙurin yin sabon zaɓen ƙananan hukumomi.

Najeriya ta taɓarɓare bayan mulkin IBB – Peter Obi An ƙwace miliyoyin daloli, gidajen da ke da alaƙa da Emefiele

A cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Alhamis, Ministan ya ce kotu ta dawo da zaɓaɓɓun shugabannin ƙananan hukumomin da aka zaɓa a ƙarƙashin tsohon Gwamna Gboyega Oyetola, amma ta tsige su ta hanyar umarnin zartarwa da gwamnan ya yi.

Fagbemi ya ce ba bisa ƙa’ida ba ne a gudanar da zaɓen ƙananan hukumomi a Osun kafin watan Oktoba lokacin da wa’adin shugabanni da kansilolin da aka zaɓa a Jam’iyyar APC zai ƙare.

Sai dai a wata sanarwa da kakakin Gwamnan, Olawale Rasheed ya fitar, gwamnan ya ce mutanen jihar a shirye suke tsaf kuma babu gudu babu ja da baya kan gudanar da zaɓen.

Ya bayyana haka ne a lokacin da yake karɓar rukunin gamayyar ƙungiyoyin farar hula da suka je jihar domin sanya ido kan zaɓen ƙananan hukumomi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gwamnan Jihar Osun zaɓen ƙananan

এছাড়াও পড়ুন:

Gidauniyar Tunawa Da Sir Ahmadu Bello Za Ta Gudanar Da Taronta Karo Na 11 A Bauchi.

Gidauniyar Tunawa Da Sir Ahmadu Bello Za Ta Gudanar Da Taronta Karo Na 11 A Bauchi.Gidauniyar Tunawa da Sir Ahmadu Bello ta sanar da cewa za ta gudanar da bikin tunawa da Sir Ahmadu Bello na shekara karo na 11 a ranar Litinin, 24 ga Fabrairu, 2025, a Bauchi, Jihar Bauchi.

Taron, wanda aka shirya tare da hadin gwiwar Gwamnatin Jihar Bauchi, zai girmama marigayi Sir Ahmadu Bello, Sardaunan Sakkwato kuma Firaministan tsohuwar Yankin Arewa.

A bana, taken laccar shi ne “Arzikin Halitta: Juya Albarkatun Yankin Arewa Zuwa Ci Gaban Tattalin Arziki Mai Dorewa.”

Tattaunawar za ta mayar da hankali ne kan yadda za a yi amfani da albarkatun noma da ma’adanai da ruwa don bunkasa ci gaban tattalin arzikin yankin.

Duba da kalubalen tattalin arzikin da Najeriya ke fuskanta, musamman yankin Arewa, laccar za ta bayyana rawar da gwamnati da ɓangarori masu zaman kansu da kungiyoyin al’umma za su taka wajen inganta sarrafa albarkatu da bunkasa darajar kayayyaki da samar da ayyukan yi.

Babbar lacca za a gabatar da ita ne daga bakin Dr. Mansur Mukhtar (Sarkin Bai Kano), tsohon Mataimakin Shugaban Bankin Musulunci kuma Shugaban Bankin Masana’antu na Najeriya.

Ana sa ran Sanata George Akume, Sakataren Gwamnatin Tarayya, zai kasance Babban Bako na Musamman a wurin taron.

Haka nan, ana sa ran halartar Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya na Jihar Gombe, wanda shi ne Shugaban Kungiyar Gwamnonin Arewa, kuma zai jagoranci taron.

Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Mohammed, zai kasance Babban Mai Masaukin baki. Haka kuma, ana sa ran halartar gwamnonin jihohi da ministoci da ‘yan majalisa da sarakuna da sauran manyan baki daga sassa daban-daban.

A cewar Darakta-Janar na Gidauniyar, Injiniya Dr Abubakar Gambo Umar, albarkatun yankin Arewa na da babban damar sauya tattalin arzikin yankin.

“Sai dai dole mu dauki matakan da za su tabbatar da sarrafa albarkatunmu cikin adalci da dorewa, domin amfanin kowa da kowa,” in ji shi.

A yayin taron, gidauniyar za ta bayar da tallafin karatu ga dalibai marasa galihu daga Jihar Bauchi da ke karatu a manyan makarantu domin tallafa musu.

Bugu da kari, za a karrama wasu fitattun mutane da lambar yabo saboda gudunmawar da suka bayar ga cigaban al’umma.

Har ila yau, za a gudanar da shirin ba da agajin lafiya domin samar da hidimar kiwon lafiya ga al’ummar yankin.

Gidauniyar Tunawa da Sir Ahmadu Bello an kafa ta ne domin ci gaba da girmama gadon shugabanci da ilimi da ci gaban tattalin arziki da marigayi Sardaunan Sakkwato ya assasa.

Bikin tunawa na kowace shekara, wanda ke gudana a jihohi 19 na Arewa, na zama wata kafa ta tattaunawa kan ci gaban yankin da shugabanci.

Gidauniyar ta nemi afuwar duk wani rashin jin dadi da sauya ranar taron ka iya haifarwa, tare da gode wa duk masu mara mata baya.

Rel: Khadija Kubau

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Adeleke Ya Kaɗa Ƙuri’a a Zaɓen Ƙananan Hukumomin Osun
  • Ɗan Abacha ya kare mahaifinsa bayan ƙaddamar da littafin IBB
  • Dalilan ƙara kuɗin Jami’ar Gombe — Gwamna Inuwa
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar Da Shirin Da’awah Na Mata A Jihar Jigawa
  • EFCC ta gargaɗi ciyamomi kan amfani da kuɗaɗen jama’a a Gombe
  • Abiola Ne Ya Lashe Zaɓen Shugaban Ƙasa Na 12 Ga Watan Yuni 1993 – Janar IBB
  • Na yi nadamar soke zaɓen 1993 — Babangida
  • Matasan Jihar Jigawa Sun Karrama Gwamna Umar Namadi
  • Gidauniyar Tunawa Da Sir Ahmadu Bello Za Ta Gudanar Da Taronta Karo Na 11 A Bauchi.