HausaTv:
2025-03-25@16:28:46 GMT

 Malaysia: An Bude Kiran Yanke Sayen Kere-kere Kamfanin “Tesla” Na Elon Musk

Published: 21st, February 2025 GMT

A kasar Malaysia an bude yin kira da a yanke kere-keren kamfanin Elon Musk saboda goyon bayan da yake nuna wa Donald Trump da siyasarsa ta son korar Falasdinawa daga Gaza.

Mutanen kasar ta Malaysia ne suke amfani da kafofin sadarwa na al’umma wajen yin kira da a yanke mu’amala da motocin da kamfanin na Telsa take kerawa saboda kusancinsa da shugaban kasar Amurka Donlad Trump wanda yake son ya tilastawa Falasdinawa daga Gaza zuwa wasu kasashe na daban.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Moscow : Dole ne Rasha da China su shiga tattaunawar nukiliya da Iran

Kasar Rasha ta bayyana cewa dole Moscow da Beijing su shiga shawarwarin tattaunawar nukiliya da Iran.

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Rasha Maria Zakharova ta bayyana cewa, Moscow a shirye take ta samar da ingantacciyar hadin gwiwa da dukkan bangarorin kan batun yarjejeniyar nukiliyar Iran. “

Shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da cewa ya aike da wasika zuwa Tehran domin fara tattaunawa kan shirin nukiliyar Iran; yayin da shi da kansa ya fice daga yarjejeniyar nukiliyar Iran a wa’adinsa na farko.

A halin da ake ciki dai ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya bayyana cewa, Jamhuriyar Musulunci ta Iran za ta mayar da martani ga wasikar shugaban Amurka Donald Trump a cikin kwanaki masu zuwa ta hanyoyin da suka dace.

Araghchi ya bayyana hakan ne a lokacin da yake jawabi kai tsaye a gidan talabijin na Jamhuriyar Musulunci ta Iran (IRIB) ranar Alhamis.

Araghchi ya kuma lura cewa a wannan karon, ci gaban ya zo tare da wani yunkuri na diflomasiyya daga Amurkawa, ciki har da wasika da bukatar yin shawarwari.

Ya kuma bayyana cewa manufar Jamhuriyar Musulunci ta Iran a bayyane take. “Ba za mu shiga tattaunawa kai tsaye karkashin matsin lamba, barazana, ko karin takunkumi.”

Ministan harkokin wajen kasar ya kuma bayyana cewa wasikar “mafi yawan barazana ce,” amma kuma akwai damamaki a ciki.

A farkon watan Maris ne Trump ya bayyana cewa ya rubuta wasika zuwa ga Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Alamar Deepseek” Ta Bude Kofar Gyara Na Kara Kunno Kai A Harkokin Duniya
  • Gwamnatin Tarayyar Najeriya Ta Kafa Rundunar Daukin Gaggawa Don Magance Matsalolin Tsaro
  • Lauyoyi 77 a Jamus sun yi kira ga gwamnati da ta mutunta sammacin ICC na cafke Netanyahu
  • Mutane Miliyan 9 Na Iya Kamuwa Da Cutar HIV Saboda Rashin Tallafi
  • Kamfanin Apple Ya Sanar Da Zuba Sabon Jari A Fannin Samar Da Makamashi Mai Tsafta A Sin
  • Duniya na ci gaba da yin tir da Isra’ila kan dawo da hare-harenta a Gaza
  • An Bude Taron Shekara-Shekara Na Dandalin Tattauna Raya Kasa Na Sin Na 2025
  • Moscow : Dole ne Rasha da China su shiga tattaunawar nukiliya da Iran
  • Isra’ila : ‘Yan adawa sun kira zanga-zangar gama-gari bayan korar shugaban Shin Bet
  •  Amurka: Turmp Yana Son Yin Yarjejeniya Ne Da Iran Ba Yaki Ba!