Wanda ya jagoranci sallar juma’a a yau a birnin Tehran  Hujjatul-Islam Wal Muslimin Muhammmad Hassan Abu Turabi Fard, ya ce; makiyan jamhuriyar musulunci ta Iran suna magana da sauti daya,yayin da juyin juya halin musulunci na Iran ya hada kasashen Lebanon,Yemen, Falasdinu,Iraki da wasu kasashen musulmi.

Limamin na Tehran ya kara da cewa, lokaci ya yi da al’ummar musulmi za su yi watsi da duk wani sabani a tsakaninsu, su dunkule su rika Magana da yawu daya.

Dangane da karatowar watan Ramadan mai alfarma, limamin na Tehran ya ce, watan Ramadan mai alfarma, wata ne na kara kulla alaka da Allah madaukakin sarki da karatun al’kur’ani.

Hujjatul Islam Wal Muslimin Abu Turabi ya kuma ce; Ma’abota alkur’ani mai girma su ne wadanda aka sani da yin rayuwa ta hankali da ilimi, kuma sakamakon wannan irin raywua shi ne samar da hadin kai da nesantar rabuwar kawuna.

Bugu da kari, limanin na Tehran ya ce hadin kai yana daga cikin sakamakon kare hakkin bil’adama, domin alkur’ani mai girma ya kiraye mu baki daya da mu kasance a tare da gaskiya da kuma tsarin musulunci.

Dangane da abinda Amurk ta mayar da hankali akansa a kiyayyarta da Iran, limamin ya ce  shi ne yakin kwakwalwa da kuma farfaganda.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: na Tehran ya

এছাড়াও পড়ুন:

Za’a Gudanar Taron Tattaunawa Tsakanin Rasha Ta Amurka A Karo Na Biyu 2 A Birnin Rayad na Kasar Saudiya

A gobe Litinin 24 ga watan Maris ne tawagogin masu tattaunawa na kasashen Amurka da Rasha zasu hadu a birnin Rayida na kasar Saudiya don ci gaba da tattaunawan da suka fara a yan makonnin da suka gabata dangane da yakin da ke faruwa a Ukraine, shekaru fiye da 3 da suka gabata, da kuma dangantaka a tsakanin kasashen biyu.

Kamfanin dillancin labaran Sputnik na kasar Rasha ya nakalto Yury Ushakov mai bawa shugaba Putin shawara kan al-amurin siyasa yana fadar haka. Ya kuma kara da cewa Sanata Georgy Karasin ne zai jagoranci tawagar masu tattaunawa ta kasar Rasha sannan ta kasar Amurka an rika an samar da tawagar, wasu zata hadu da na Rasga a gobe litin a birnin Riyad.

Kafin haka dai shugaban kasar Rasha Vladimir Putin sun tattauna da tokwaransa na kasar Amurka Donal Trump kan al-amura da dama wadanda suka shafi yakin a Ukraine da tsagaita budewa juna wuta na wata guda da kuma wasu al-amura.

Karsin daga karshe ya ce yana fatan tattaunawan zata yi armashi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Turkiyya Sun Bukaci kasashen Musulmi Su Magance matsalar Jinkai A Kasar Palasdinu Da Aka Mamaye
  • Rasha ta ce tana nazari kan sakamakon tattaunawar
  • Wajibcin Gina Al’ummar Duniya Mai Kyakkyawar Makomar Bai Daya
  • Babban Kusa A Kungiyar Hamas Salah Al-Bardawil Ya Yi Shahada
  • Za’a Gudanar Taron Tattaunawa Tsakanin Rasha Ta Amurka A Karo Na Biyu 2 A Birnin Rayad na Kasar Saudiya
  • Tunanin Raya Al’ummar Dan Adam Zai Tabbatar Da Makoma Mai Haske Ga Kowa
  • Moscow : Dole ne Rasha da China su shiga tattaunawar nukiliya da Iran
  • Araghchi : Ya kamata Duniyar Musulmi ta dauki mataki mai karfi kan Isra’ila
  • Wang Yi: Kasar Sin Na Da Kwarin Gwiwa Kan Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Japan Da Koriya Ta Kudu  
  • Kao Kim Hourn: Ba Ta Hanyar ‘Siddabaru’ Kasar Sin Ta Cimma Nasarori A Fannin Ci Gaba Ba Sai Dai Ta Hanyar Aiki Tukuru Kuma Mai Dorewa