Ma’aikatan Gidan Rediyon Tarayya (FRCN) da na Hukumar Gidan Talabijin ta Najeriya (NTA) da suka yi ritaya, sun bayyana jin dadinsu kan karin haske da Ministar Kudi ta yi game da wadanda za su ci gajiyar Naira Biliyan 758 da aka amince da su don biyansu kudaden fansho da suke bi.

A tsokacin da suka yi game da lamarin a Kaduna, ’yan fanshon sun bayyana cewa, bayanin ya tabbatar da cewa za a raba kudaden ne zuwa sassa biyu na ma’aikatan da suka yi ritaya a karkashin hukumar fansho ta PTAD da kuma shirin bayar da gudunmawar fansho (CPS).

Sun bayyana fatan cewa za a biya kudaden kafin karshen watan da ake ciki, domin baiwa ‘yan fansho damar gudanar da azumin watan Ramadan cikin kwanciyar hankali da walwala.

Tsohon babban jami’in tsaro na NTA, Alhaji Abdullahi Umar, ya yabawa gwamnatin tarayya bisa wannan tabbacin da ta bayar, ya kuma bukaci kungiyoyin ‘yan fansho da su sanya ido sosai kan yadda ake biyan kudaden domin kaucewa duk wata matsala.

Ya kuma yi kira da a saka ‘yan fansho a cikin shirin inshorar lafiya na kasa (NHIS), wanda a baya aka dawo da shi, domin a taimaka musu wajen kula da lafiyarsu.

 

Suleiman Kaura

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Babban Kwamandan IRGC Ya Bayyana Cewa: Amurka Da Isra’ila Ba Su Yi Nasara A Yakin Gaza Ba

Babban kwamandan dakarun kare juyin juya halin Musulunci ya bayyana cewa: Amurka da gwamnatin ‘yan Sahayoniyya ba su yi nasara a yakin da suka kaddamar kan ‘yan gwagwarmaya a Gaza ba

Babban kwamandan dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran Manjo Janar Hossein Salami ya jaddada cewa: Haramtacciyar kasar Isra’ila ba za ta samu wanzuwa idan babu Amurka, yana mai cewa, ita kanta Amurka ta kama hanyar rugujewa. Ya kara da cewa: Wadannan al’amura suna faruwa ne a kasa kuma wani bangare ne na makomar al’umma, don haka wajibi ne al’umma su dogara ga Allah kuma su yi duk abin da za su iya.

A yayin ganawarsa da Ziyad al-Nakhala babban sakataren kungiyar Jihadul-Islami, Manjo Janar Salami ya yi nuni da irin nasarorin da dakarun gwagwarmayar Falastinawa da al’ummar Gaza suka samu a kan yahudawan sahyoniya ‘yan mamaya, yana mai bayyana wannan nasara a matsayin nasara da take a fili kuma nasara ce bayyananniya ta Ubangiji” wacce ta kawo abin alfahari ga duniyar Musulunci, yayin da Allah ya girmama Falastinawa da nasara bayan tsawon shekaru ana killace da su saboda matakan zalunci.

Babban kwamandan dakarun kare juyin juya halin Musuluncin ya kara da cewa: Zafin zalunci da wahalhalun da al’ummar Falastinu suke sha yana damun kowa a cikin zukata duk jurewa hakan yana da wahala da wuya, amma al’umma tana godiya ga Allah kasancewa wadannan al’amura sun kare da nasarar da jarumai a Gaza suka samu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sanata Katung ya bayyana damuwa kan ƙaruwar ta’addanci a kudancin Kaduna
  • Kallon-Kallo: Ƙungiyar Ƙwadago Da ‘Yan Nijeriya
  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Dauki Nauyin Dalibai 80 Da Ke Manyan Makarantu
  • Turji Ya Ƙaƙaba Wa Ƙauyen Mataimakin Gwamnan Sokoto Da Wasu Biyan Harajin Miliyan 22
  • Tsarin Fansho Na Jihar Jigawa Ya Yi Wa Sauran Jihohi Zarra- Premium Pension
  • Karyewar Farashi: Ba mu shigo da kayan abinci daga waje ba — Minista
  • Babban Kwamandan IRGC Ya Bayyana Cewa: Amurka Da Isra’ila Ba Su Yi Nasara A Yakin Gaza Ba
  • Shugaba Tinubu Ya Yaba Da Gudunmawar Da IBB Ya Bayar Yayin Mulkinsa
  • Harin ’Yan bindiga: Mun yi asarar shanu sama da miliyan 4 – Miyetti Allah